Gwamnatin Tarayya ta ba da sanarwar naɗin Ambasada Isma’il Yusuf Abba a matsayin sabon Shugaban Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON), bisa jiran amincewar Majalisar Dattawa.
Wannan na zuwa ne bayan murabus ɗin Farfesa Abdullahi Saleh Usman a ranar Litinin.
An ba da sanarwar wannan sabon naɗi a yau.
Mataimakiyar Darakta, Sashen Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na NAHCON, Hajiya Fatima Sanda Usara, ta bayyana cewa Yusuf, wanda tsohon jami’in diflomasiyya ne a Ma’aikatar Harkokin Waje, shi ne Jakadan Nijeriya na baya-bayan nan a ƙasar Turkiyya.
An haife shi a ranar 7 ga Yuli, 1962 a Mubi, Jihar Adamawa. Ya kammala karatu a Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo da ke Sakkwato a shekarar 1985 inda ya samu digiri a fannin Kimiyyar Siyasa.
Ya yi hidimar ƙasa (NYSC) a Cibiyar Kasuwanci, Masana’antu, Ma’adanai da Noma ta Ijebu a 1986, sannan nan take aka ɗauke shi aiki a Ma’aikatar Harkokin Waje a Disamban 1986.
Yusuf ya halarci manyan kwasa-kwasan ƙwarewa, kuma ya kai matsayi Darakta a shekarar 2013.
Daga bisani, a 2021 aka naɗa shi Jakada Mai Cikakken Iko kuma Na Musamman a Jamhuriyar Turkiyya.
Usara ta ce: “Ambasada Yusuf ya taka muhimmiyar rawa wajen hanzarta dangantakar dabaru da Turkiyya, musamman a fannonin tsaro, kare ƙasa, kasuwanci da zuba jari, da haɗin gwiwar masana’antu.”
Ta ƙara da cewa ƙwarewar sa ta ginu ne kan gogewa mai tsawo ta tsawon shekaru 35 na aikin gwamnati da aka rubuta a tarihi.
A tsawon zamanin aikin sa, ya yi aiki a ofisoshi daban-daban, ciki har da ofisoshin jakadancin Nijeriya a Ajantina, Italiya da Chana.
A hedikwata kuwa, ya riƙe muƙamai daban-daban a sassa kamar nazari, ayyuka, horaswa, gudanarwa, da kuma harkokin alhazai, inda ya jagoranci sakatariyar Kwamitocin Shugaban Ƙasa kan Hajji (PCH) daga 2002 zuwa 2007.
Kwamitin PCH yana da alhakin ƙirƙiro, tsara da aiwatar da ingantattun manufofi domin tabbatar da tafiyar aikin Hajji cikin sauƙi ga Musulman Nijeriya zuwa Saudiyya a kowace shekara.
Ayyukan kwamitin ne suka shimfiɗa tubali da tsarin kafa NAHCON da kuma fara aikin ta cikin nasara a 2006, inda Yusuf ya kuma yi aiki a matsayin sakataren jadawalin ayyuka.
Tun da fari a 2005, ya kasance sakataren wata babbar tawagar Gwamnatin Tarayya da ta je nazarin yadda ake gudanar da harkokin Hajji a Malesheya da Indonesiya.
An yi hakan ne bisa ga gagarumar ƙwarewa da ingancin da ƙasashen biyu suka nuna a harkokin Hajji tsawon shekaru.
Sakamakon binciken tawagar ya ba da gudunmawa sosai ga farkon ayyukan NAHCON, musamman wajen kafa Tsarin Ajiya na Hajji (Hajj Savings Scheme).
Yusuf ya kuma kasance Sakataren tawagogin Gwamnatin Tarayya guda biyu (Amirul Hajj) a shekarun 2012 da 2013.
Daga 2011 zuwa 2013, bayan an tura shi Fadar Shugaban Ƙasa, ya yi aiki a matsayin Mataimaki na Musamman kan Harkokin Shugaban Ƙasa a ofishin Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa (Chief of Staff). Ayyukan sa sun haɗa da taƙaita da nazarin takardun bayanai (memos), da kuma taimaka wa Shugaban Ma’aikata wajen tsara shirye-shiryen Shugaban Ƙasa.
Ambasada Yusuf yana jin harsunan Hausa, Yarbanci, Igala, Turanci da Sifaniyanci.
Usara ta ce shugabannin NAHCON sun yi maraba da wannan sabon naɗi, tare da bayyana shirin su na bai wa sabon shugaban cikakken goyon baya, sannan ta buƙaci ma’aikata da masu ruwa da tsaki da su ba da haɗin kai da goyon baya.
“Wannan yana da matuƙar muhimmanci musamman a daidai lokacin da shirye-shiryen aikin Hajjin bana suka kai wani mataki na gaba,” inji ta.







