Gwamnatin Nijeriya da Tarayyar Turai (EU) sun ƙaddamar da wani sabon shiri na ilimi da ƙarfafa wa matasa gwiwa mai darajar Yuro miliyan 40 domin inganta harkar ilimi a yankin Arewa-maso-yamma na ƙasar nan.
An gudanar da taron ne a Abuja, inda Babban Sakataren Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Abel Olumuyiwa Enitan, wanda Dakta Ejeh Usman ya wakilta, ya bayyana shirin a matsayin ginshiƙin manufar ‘Renewed Hope Agenda’ ta Shugaba Bola Ahmed Tinubu da kuma ‘Education Sector Renewal Initiative’ da ke nufin tabbatar da dama ga kowa wajen samun ingantaccen ilimi.
Shugabar sashen ilimi na matakin farko, Dakta (Mrs) Folake Davies Olatunji, ta ce shirin zai mayar da hankali ne wajen koyar da ilimi tun daga tushe, horar da malamai, inganta ilimin zamani ta hanyar fasaha da kuma bayar da damar ilimi ga kowa.

A nata jawabin, wakiliyar EU, Miss Kate Kanebi, ta tabbatar da jajircewar Tarayyar Turai, inda ta bayyana cewa kuɗin da ya kai naira biliyan 69.9 za su taimaka wajen samar da tsare-tsaren karatu cikin aminci, koyar da sana’o’in dogaro da kai musamman ga mata da marasa galihu.
Cibiyoyi irin su UBEC, TRCN, UNESCO, UNICEF, Plan International, Save the Children da kuma Bankin Duniya sun halarci taron.
A ƙarshe, taron ya kammala da alƙawari haɗin gwiwa wajen tabbatar da ilimi mai inganci da ya shafi kowa a faɗin ƙasar nan.







