Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta ba da sanarwar buɗe shafin neman aiki domin ɗaukar Masu Koyar da Sana’o’in Fasaha (Technical Facilitators) a Kwalejojin Fasaha na Gwamnatin Tarayya da ke faɗin ƙasar nan, a wani mataki na musamman na tsawon shekara guda domin farfaɗo da tsarin koyar da sana’o’i.
Ma’aikatar ta ce wannan shiri yana daga cikin manufofin Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da nufin cike gibin ƙwarewar sana’o’i a Nijeriya ta hanyar jawo ƙwararrun masana daga fannoni daban-daban na sana’a da masana’antu domin koyar da ilimin zamani bisa ƙa’idojin ƙwarewa (competency-based training).
Sanarwar ta ce ana neman ƙwararrun masana fasaha masu ƙwarewa tare da iya koyarwa, domin inganta koyar da darussa na aikace-aikace da na ƙa’ida a Kwalejojin Fasaha na Tarayya.
Wannan shiri yana daga cikin sauye-sauyen da gwamnati ke aiwatarwa domin tabbatar da cewa ilimin fasaha ya dace da buƙatun kasuwar aiki ta zamani.
Ma’aikatar ta buƙaci duk masu sha’awar neman aikin da su cike takardar neman aiki ta yanar gizo ta shafin da aka bayar.
Ta jaddada cewa za a tantance dukkan rajistar da aka tura bisa cancanta da ƙwarewa.
An sanar da cewa za a rufe shafin neman aikin da ƙarfe 11:59 na dare a ranar Litinin, 16 ga Maris, 2026.
Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta sake jaddada ƙudirin ta na mayar da Kwalejojin Fasaha na Tarayya cibiyoyin ƙwarewa wajen haɓaka sana’o’i, ƙirƙire-ƙirƙire da shirya matasa domin samun aiki.







