• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Ilimi

Gwamnatin Tinubu ta buɗe shafin ɗaukar ma’aikatan koyar da sana’o’i a Kwalejojin Fasaha

Wakilin Mu by Wakilin Mu
February 18, 2026
in Ilimi
A A
0
Gwamnatin Tarayya ta fara horas da matasa 260,000 a fannoni daban-daban na sana’o’in dogaro da kai
Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa

Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa

Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta ba da sanarwar buɗe shafin neman aiki domin ɗaukar Masu Koyar da Sana’o’in Fasaha (Technical Facilitators) a Kwalejojin Fasaha na Gwamnatin Tarayya da ke faɗin ƙasar nan, a wani mataki na musamman na tsawon shekara guda domin farfaɗo da tsarin koyar da sana’o’i.

Ma’aikatar ta ce wannan shiri yana daga cikin manufofin Renewed Hope Agenda na Shugaba Bola Ahmed Tinubu, da nufin cike gibin ƙwarewar sana’o’i a Nijeriya ta hanyar jawo ƙwararrun masana daga fannoni daban-daban na sana’a da masana’antu domin koyar da ilimin zamani bisa ƙa’idojin ƙwarewa (competency-based training).

Sanarwar ta ce ana neman ƙwararrun masana fasaha masu ƙwarewa tare da iya koyarwa, domin inganta koyar da darussa na aikace-aikace da na ƙa’ida a Kwalejojin Fasaha na Tarayya.

Wannan shiri yana daga cikin sauye-sauyen da gwamnati ke aiwatarwa domin tabbatar da cewa ilimin fasaha ya dace da buƙatun kasuwar aiki ta zamani.

Ma’aikatar ta buƙaci duk masu sha’awar neman aikin da su cike takardar neman aiki ta yanar gizo ta shafin da aka bayar.

Ta jaddada cewa za a tantance dukkan rajistar da aka tura bisa cancanta da ƙwarewa.

An sanar da cewa za a rufe shafin neman aikin da ƙarfe 11:59 na dare a ranar Litinin, 16 ga Maris, 2026.

Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta sake jaddada ƙudirin ta na mayar da Kwalejojin Fasaha na Tarayya cibiyoyin ƙwarewa wajen haɓaka sana’o’i, ƙirƙire-ƙirƙire da shirya matasa domin samun aiki.

Tags: KwalejinFasahaMa'aikatarIlimisana'a
Previous Post

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da taraktoci 2,000 domin noma hekta miliyan 1.5

Next Post

Gwamnan CBN ya bayyana alfanun bai wa Nijeriya kujerar dindindin a Hukumar Gudanarwar Cibiyar Kuɗi ta Afrika

Related Posts

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya
Ilimi

Ku daina kira na Bahaushe, cewar Bishop Kukah ga ’yan Nijeriya

April 26, 2026
NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795
Ilimi

NELFUND ta biya wa ɗalibai 6,385 na Jami’ar Lafiya kuɗin makaranta naira miliyan 795

April 19, 2026
Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi
Ilimi

Gwamnatin Kano ta haɗe Ma’aikatar Ilimi Mai Zurfi da Ma’aikatar Ilimi

March 15, 2026
Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista
Ilimi

Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista

January 24, 2026
Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano
Ilimi

Abin burgewa: Sarki Sanusi ya fara halartar lacca a matsayin ɗalibin jami’a a Kano

January 20, 2026
Gwamnatin Tarayya ta buɗe rajistar neman guraben karatu a ƙasar waje na PTDF
Ilimi

Gwamnatin Tarayya ta buɗe rajistar neman guraben karatu a ƙasar waje na PTDF

January 20, 2026
Next Post
Tarayyar Turai ta bi sahun Hukumar FATF, ta cire Nijeriya daga jerin ƙasashen da ke da haɗarin safarar kuɗi

Gwamnan CBN ya bayyana alfanun bai wa Nijeriya kujerar dindindin a Hukumar Gudanarwar Cibiyar Kuɗi ta Afrika

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!