Nijeriya a ranar Litinin ta bi sahun yawancin ƙasashen duniya wajen kaɗa ƙuri’a domin goyon bayan wani ƙudiri da ke sake jaddada haƙƙin Falasɗinawa na kafa ƙasar su ta kan su.
Babbar Taron Majalisar Ɗinkin Duniya ya kaɗa ƙuri’a tare da amincewa da ƙudirin da ke tabbatar da haƙƙin kafa ƙasar Falasɗinu mai cin gashin kan ta.
Jimillar ƙasashe membobi 164, ciki har da dukkan ƙasashen Afrika 54 da ke cikin Majalisar Ɗinkin Duniya, sun kaɗa ƙuri’ar goyon bayan ƙudirin.
Gaba ɗaya, ƙasashe takwas ne kawai suka kaɗa ƙuri’ar adawa da ƙudirin. Waɗannan su ne: Isra’ila, Amurka, Micronesia, Argentina, Paraguay, Papua New Guinea, Palau, da Nauru.
Ƙudirin ya sake jaddada matsayar Majalisar Ɗinkin Duniya da aka daɗe a kan ta, wadda ke tabbatar da haƙƙin al’ummar Falasɗinu na kafa ƙasar su da kuma bin ci gaban tattalin arziki, zamantakewa da al’adu.
Haka kuma, ƙudirin ya yi kira ga dukkan ƙasashe, hukumomi na musamman na Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran sassan tsarin MDD da su ci gaba da ba da goyon baya da taimako ga al’ummar Falasɗinu domin a hanzarta tabbatar da wannan haƙƙi.
Ya kuma jaddada buƙatar mutunta haɗin kai na yanki, ci gaba da jere-jeren ƙasa da cikakken ikon yankunan Falasɗinu da aka mamaye, ciki har da Gabashin Ƙudus.
Wannan ƙudiri ya zo ne kwanaki kaɗan bayan Majalisar Ɗinkin Duniya ta goyi bayan wani ƙudiri da ke buƙatar Isra’ila ta ɗage takunkumin da ta ƙaƙaba kan isar da agajin jinƙai zuwa Zirin Gaza.
Majalisar ta kuma buƙaci Isra’ila da ta dakatar da kai hare-hare kan wuraren Majalisar Ɗinkin Duniya, tare da bin dokokin ƙasa da ƙasa, bisa la’akari da wajibcin ta a matsayin ta na ƙasar mamaya.
Sai dai Jakaden Isra’ila a Majalisar Ɗinkin Duniya, Danny Danon, ya zargi majalisar da amincewa da wani ƙudiri da ke tilasta Isra’ila yin aiki da ta’addanci.
Firayim Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya daɗe yana ƙin amincewa da kafa ƙasar Falasɗinu.
Nijeriya tana daga cikin ƙasashen da suka sha yin kira da a samar da tsarin ƙasashe biyu domin kawo ƙarshen yaƙin Isra’ila da Hamas, wanda ya yi sanadin mutuwar dubban Falasɗinawa.
A Babban Taron Majalisar Ɗinkin Duniya da aka gudanar a watan Satumba, Mataimakin Shugaban Ƙasar Nijeriya, Kashim Shettima, ya ce dole ne a bai wa Falasɗinawa ’yanci da mutunci iri ɗaya da wanda ake bai wa sauran ’yan ƙasashen duniya.
Yayin da yake jawabi a gaban majalisar, Shettima ya ce al’ummar Falasɗinu ba su cancanci ci gaba da fuskantar rikice-rikice na dogon lokaci da kuma mummunan bala’in jinƙai da suka sha ba.
“Su ma mutane ne, daidai daraja, kuma sun cancanci irin ’yanci da mutunci da muke ɗauka a matsayin abu na kowa,” inji shi.
A yayin taron, wasu ƙasashen Turai da dama, ciki har da Birtaniya, Kanada da Ostiraliya, sun amince da Falasɗinu a hukumance a matsayin ƙasa mai cin gashin kan ta.
Cikin fushi, Mista Netanyahu ya bayyana matakin nasu a matsayin “kyautar banza ga ta’addanci.”
Ya sha alwashin cewa “ba za a kafa Ƙasar Falasɗinu a yammacin Kogin Jodan ba.”
Ya kuma ce Isra’ila za ta ci gaba da yaƙi a Majalisar Ɗinkin Duniya da sauran dandalin ƙasa da ƙasa domin tunkarar abin da ya kira da “ƙaryar farfaganda.”







