A yayin da Hausawa mazauna birnin Legas ke tsakiyar kukan rushe sanannar kasuwar da suke hada-hada, wato Alaba, a gefe ɗaya kuma Gwamnatin Jihar Legas ta buɗe katafariyar masana’antar sarrafa fatun dabbobi.
Rahotanni sun nuna a ƙarshen makon da ya gabata ne dai Uwargidan Shugaban Najeriya, Remi Tinubu ta ƙaddamar da wata sabuwar masana’antar sarrafa fatar dabbobi a Mushin, da ke Legas, wadda za ta samar da ayyukan yi sama da 10,000. A wannan wuri an samar da na’urorin zamani, waɗanda za’a dinga sarrafa fatun dabbobi, ana yin jakankuna da takalma da kuma kayyaki daban daban da ake yi da fata.
Gwamnan Jihar Legas, Sanyo Olu ya jaddada cewa jihar sa za ta riƙa samun cinikin Naira sama da biliyan 350 duk shekara, ta hanyar fitar da fatun dabbobi zuwa ƙasashen waje.
A gefe ɗaya kuma Hausawan da aka tarwatsa daga Kasuwar Alaba, sun yi kukan cewa Gwamnatin Jihar Legas ta ci amanar su, domin su ne suka kafa kasuwar.

Sun ce da can wurin daji ne kuraye, nacizai har ma da zaki. Sun ce a cikin 1978 suka gyara wurin tare da cike kwatami-kwatamin wuraren da ruwa ke taruwa, suka kafa kasuwa.







