Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bada umurnin cewa Dakta Salihu Abdulhamid Dembos, wato Darakta-Janar na Hukumar Talbijin ta Nijeriya (NTA) wanda aka sauke kwanan nan, ya koma kan muƙamin sa.
Idan kun tuna, kwanan nan aka bada sanarwar tsige Dembos daga kujerar sa sakamakon wasu canje-canje da aka yi a hukumar.
Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Yaɗa Labarai, Bayo Onanuga, shi ne ya bayyana hakan a cikin sanarwa ga manema labarai a ranar wannan Talatar.
Shi dai Dembos, Shugaba Buhari ne ya naɗa shi, sannan Shugaba Tinubu ya sake naɗa shi a cikin Oktoba 2023.
Ana sa ran zai ci gaba ya ƙarasa wa’adin sa na shekaru uku.

Bugu da ƙari, Shugaba Tinubu ya bada umurnin dawo da Mista Ayo Adewuyi a matsayin sa na Babban Daraktan Labarai na NTA domin ya ƙarasa wa’adin sa na shekaru uku da zai ƙare a cikin 2027.
Tinubu ne ya naɗa shi muƙamin a cikin 2024.
Wato dai wannan sabon umurnin ya soke naɗe-naɗen da aka yi kwanan nan na darakta-janar, babban daraktan labarai, daraktan kasuwanci, da manajan daraktan kamfanin NTA Enterprises.







