* Ya Ƙaddamar Da Wasu Hanyoyin
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga ‘yan Nijeriya da su ƙara haƙuri kan halin da ake ciki domin jin daɗi yana nan tafe.
Ya faɗi haka ne a yau Asabar lokacin da yake ƙaddamar da babban titin bakin teku da ya tashi daga Legas zuwa Kalaba, tare da shan alwashin cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da aiwatar da shirye-shirye domin amfanuwar ‘yan Nijeriya.
Ya ce: “Ina roƙon dukkan ‘yan Nijeriya kan cewa kyakkyawar fata tana tare da mi. Tattalin arzikin mu yana farfaɗowa.”
Ya yi nuni da yadda ake samun daidaito a musanyar kuɗi sannan kuma farashin kayan abinci yana raguwa.
Haka kuma shugaban ya ƙaddamar da wasu manyan hanyoyin a faɗin ƙasar nan.
A bikin ƙaddamarwar wanda aka yi a Legas a yau, Tinubu ya umarci Ministan Ayyuka, David Umahi, da sauran ministoci da ke kula da ayyukan da ake aiwatarwa a sassan ƙasar nan da su riƙa bin dokar nan da ta gindaya sharaɗin yin amfani da kayan aikin da ake da su cikin ƙasar, da horas da ‘yan Nijeriya da kuma sauyin fasaha.

Gwamnonin jihohin Legas, Delta, Ogun, Edo, Bayelsa, Borno, Ekiti, Kogi, Ondo, Kuros River, da Imo sun halarci taron.
Babban marubuci, Farfesa Wole Soyinka, da Mashawarcin Shugaban Ƙasa kan Tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ‘ya’yan Chagoury, da ‘yan kwangilar hanyar su ma sun halarta.
Manyan ‘yan kasuwa irin su Aliko Dangote, Abdulsamad Rabiu, da Ciyaman ɗin UBA Group, Tony Elumelu, sun halarta.







