• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Friday, May 15, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa

New Citizen Hausa by New Citizen Hausa
May 30, 2025
in Labarai
A A
0
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa
Alhaji Mohammed Idris, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai

Alhaji Mohammed Idris, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai

GWAMNATIN Tarayya ta bayyana alhini bisa ambaliyar da ta auka wa garin Mokwa a Jihar Neja, wadda ta yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da raba ɗaruruwan jama’a da muhallan su.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana da cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya samu cikakken bayani kan halin da ake ciki kan wannan ibtila’in, kuma ya umurci dukkan hukumomin agaji da na tsaro da su ƙara zage dantse wajen gudanar da ayyukan ceto da agaji.

Ya ce: “Tunani da addu’o’in mu suna tare da iyalan da suka rasa ‘yan’uwan su da kuma duk waɗanda ambaliyar ta shafa.”

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) tare da haɗin gwiwar Sojojin Nijeriya da Gwamnatin Jihar Neja suna aiki ba dare ba rana wajen kai ɗauki ga waɗanda abin ya shafa.

Gwamnatin Tarayya ta yaba da jarunta da sadaukarwar jami’an farko da masu aikin sa kai da ke ci gaba da sanya rayuwar su cikin haɗari don ceton wasu.

Hukumomi na roƙon mazauna yankunan da ambaliya ta shafa da su bi umarnin kwashe jama’a daga yankunan da ke cikin haɗari tare da haɗa kai da jami’an agaji don tabbatar da tsaron lafiyar kowa da kowa.

A cikin sanarwar, Gwamnatin Tarayya ta miƙa saƙon ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu, tare da jaddada cewa al’ummar ƙasar nan suna tare da su a wannan lokaci na jimami, kuma ba za a yi ƙasa a gwiwa wajen tallafa masu ba.

Previous Post

Sauye-sauyen da na kawo sun fara haifar da ɗa mai ido – Tinubu a jawabin cika shekaru biyu

Next Post

Ku Ƙara Haƙuri, Cewar Tinubu Yayin Ƙaddamar Da Kashin Farko Na Titin Bakin Teku Na Legas Zuwa Kalaba

Related Posts

Kotu a Amurka ta ɗaure farfesa ‘yar Nijeriya watanni 70 kan satar dala miliyan 1.4
Labarai

Kotu a Amurka ta ɗaure farfesa ‘yar Nijeriya watanni 70 kan satar dala miliyan 1.4

May 14, 2026
EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Next Post
Ku Ƙara Haƙuri, Cewar Tinubu Yayin Ƙaddamar Da Kashin Farko Na Titin Bakin Teku Na Legas Zuwa Kalaba

Ku Ƙara Haƙuri, Cewar Tinubu Yayin Ƙaddamar Da Kashin Farko Na Titin Bakin Teku Na Legas Zuwa Kalaba

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!