Firayim Ministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya ce ƙasar sa tana aiki kan wata ajanda domin tallafa wa al’ummomin Kirista “da ke fama da matsin lamba a Nijeriya.”
Netanyahu ya bayyana hakan ne a yau Juma’a yayin wani taro da shugabannin al’ummar Kiristoci masu wa’azi a jihar Florida ta ƙasar Amurka, inda ya bayyana Isra’ila a matsayin ƙasar da ita kaɗai ce ke da ikon kare Kiristoci a duniya.
Ya ce: “Na ga yaƙin da ake yi da mu da kuma yaƙin da ake yi da al’adar Yahudawa da Kiristoci, wanda a zahiri ana gwabzawa a duk faɗin duniya. Kuma ana gwabza shi ne musamman ta hannun ƙarfi biyu — Musuluncin Shi’a mai tsattsauran ra’ayi da kuma Musuluncin Sunni mai tsattsauran ra’ayi.
“Wannan na nufin gungun da Iran ke jagoranta, wanda aka raunana sosai, gaskiya ne, amma har yanzu yana nan, da kuma gungun Sunni da ƙungiyar Muslim Brotherhood ke jagoranta, wadda ta kutsa cikin komai.
“Suna zuwa Turai, suna zuwa Amurka, suna zuwa Afrika, Nijeriya. Kuma muna sane da gaskiyar cewa ana tsananta wa Kiristoci — a faɗin Gabas ta Tsakiya, a Siriya, a Lebanon, a Nijeriya, a Turkiyya da ma bayan haka.
“Muna kuma sane da gaskiyar, kamar yadda ku ma kuka sani, cewa ƙasa ɗaya ce kawai ke kare al’ummar Kirista — tana ba su damar bunƙasa, tana kare su, tana tabbatar da cewa suna ci gaba — kuma wannan ƙasar ita ce Isra’ila. Babu wata ƙasa daban. Babu ko ɗaya.
“Muna shiga wani ƙoƙari na kafa, a zahiri, ƙungiyar ƙasashe ko ƙasashen da ke tallafa wa al’ummomin Kirista a duk duniya — al’ummomin da ke cikin hali na matsi waɗanda suka cancanci taimakon mu.
“Kamar yadda kuke taimaka mana, mu ma muna son mu taimaka muku; kuma muna da ikon yin haka. A Afrika, ta hanyar bayanan sirri, a Gabas ta Tsakiya kuma da hanyoyi da dama da ba zan lissafa su ɗaya bayan ɗaya ba.
“Wannan ita ce ajandar mu; muhimmin ɓangare ne na ajandar mu.”
Jawaban na Netanyahu sun zo ne kwana guda bayan ganawar sa da Shugaban Amurka Donald Trump, wanda ya bada sanarwar kai hare-haren sama a Nijeriya a ranar Kirsimeti domin cika barazanar sa ta tsoma bakin soja don dakatar da abin da ya kira tsananta wa Kiristoci a ƙasar.
A ranar da aka kai hare-haren, Netanyahu ya ce dole ne a kawo ƙarshen hare-haren da ake kai wa Kiristoci a Nijeriya.
Isra’ila ita ce kaɗai ƙasar da ta fito fili ta goyi bayan Amurka kan iƙirarin da ta yi na “matsa wa Kiristoci” a Nijeriya.
Dukkan ƙasashen biyu an san su da kasancewa abokan ƙawance na ƙut da ƙut da juna.







