• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Harin Borno: Tinubu ya umurci hukumomin tsaro su ƙara sa ido – Shettima

Wakilin Mu by Wakilin Mu
December 25, 2025
in Labarai
A A
0
Gwamnatin Tarayya Za Ta Gaggauta Bayar Da Lamunin Naira Biliyan 250 Ga Manoma
Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a taron

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, a taron

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce Gwamnatin Tarayya na tura ƙarin ƙungiyoyin tsaro na musamman zuwa yankin da ‘yan ta’adda suka kai hari a Maiduguri, domin bibiyar su tare da cafke waɗanda ke da alhakin harin.

Shettima ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, inda ya yi Allah-wadai da fashewar bam ɗin da ta yi sanadin mutuwar mutane biyar tare da jikkata wasu da dama a wani masallaci da ke Kasuwar Gamboru, Maiduguri, a ranar Laraba.

Mataimakin shugaban ƙasar ya bayyana harin a matsayin “mummunan hari kan fararen hula marasa laifi da kuma zaman lafiyar ƙasa.”

Ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin ƙara tsaurara ayyukan tsaro nan take a Jihar Borno, biyo bayan faruwar lamarin.

Ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya na aiki kafaɗa da kafaɗa da gwamnatin jihar da kuma hukumomin tsaro na ƙananan hukumomi, domin tabbatar da kare al’umma masu rauni da muhimman kayayyakin more rayuwa a duk faɗin Arewa maso Gabas da sauran sassan ƙasar.

Ya ce, “Gwamnatin Tarayya ba za ta amince da duk wani yunƙuri na tauye zaman lafiya da tsaron ƙasar mu ba.

“Hukumomin tsaron mu na aiki dare da rana domin tabbatar da cewa waɗanda suka aikata wannan mummunan laifi an gurfanar da su gaban shari’a cikin gaggawa.”

Shettima ya bayyana ƙwarin gwiwar sa cewa tsarin tsaron da ake da shi a halin yanzu ba kawai zai cafke masu laifin ba, har ma zai fayyace dukkan yanayin da ya kewaye faruwar lamarin.

Ya ce, “Muna jajanta wa Gwamnatin Jihar Borno, mazauna jihar da kuma iyalan da suka rasa ‘yan’uwan su a wannan hari.

“Gwamnatin Tarayya na da yaƙinin cewa waɗanda ke da alhakin wannan abin ƙyama na ta’addanci za su fuskanci cikakken hukuncin doka.”

Ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa jajircewar gwamnatin Tinubu wajen kare tsaron ƙasa, bisa tanadin kundin tsarin mulki, ba za ta ja da baya ba.

“Tun bayan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya hau mulki a shekarar 2023, wannan gwamnati ta ci gaba da jaddada ƙudirin ta na kare tsaro, haɗin kai da kwanciyar hankali na ƙasar mu.

“Wannan ƙudiri na nan daram ƙarƙashin Allah da Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Jamhuriyar Nijeriya.

“Za mu ci gaba da bai wa hukumomin tsaro dukkan albarkatun da tallafin da suke buƙata domin murƙushe ta’addanci a kowane irin salo,” inji shi.

Tags: hariKashim ShettimaMaidugurita'addancitsaro
Previous Post

Yadda fashewar bam ta kashe masallata a masallaci a Maiduguri – ‘Yan sanda

Next Post

Tinubu ya taya tsohon shugaban APC, Ganduje murnar cika shekaru 76

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Tinubu ya taya tsohon shugaban APC, Ganduje murnar cika shekaru 76

Tinubu ya taya tsohon shugaban APC, Ganduje murnar cika shekaru 76

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!