Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce Gwamnatin Tarayya na tura ƙarin ƙungiyoyin tsaro na musamman zuwa yankin da ‘yan ta’adda suka kai hari a Maiduguri, domin bibiyar su tare da cafke waɗanda ke da alhakin harin.
Shettima ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, inda ya yi Allah-wadai da fashewar bam ɗin da ta yi sanadin mutuwar mutane biyar tare da jikkata wasu da dama a wani masallaci da ke Kasuwar Gamboru, Maiduguri, a ranar Laraba.
Mataimakin shugaban ƙasar ya bayyana harin a matsayin “mummunan hari kan fararen hula marasa laifi da kuma zaman lafiyar ƙasa.”
Ya ce Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar da umarnin ƙara tsaurara ayyukan tsaro nan take a Jihar Borno, biyo bayan faruwar lamarin.
Ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya na aiki kafaɗa da kafaɗa da gwamnatin jihar da kuma hukumomin tsaro na ƙananan hukumomi, domin tabbatar da kare al’umma masu rauni da muhimman kayayyakin more rayuwa a duk faɗin Arewa maso Gabas da sauran sassan ƙasar.
Ya ce, “Gwamnatin Tarayya ba za ta amince da duk wani yunƙuri na tauye zaman lafiya da tsaron ƙasar mu ba.
“Hukumomin tsaron mu na aiki dare da rana domin tabbatar da cewa waɗanda suka aikata wannan mummunan laifi an gurfanar da su gaban shari’a cikin gaggawa.”
Shettima ya bayyana ƙwarin gwiwar sa cewa tsarin tsaron da ake da shi a halin yanzu ba kawai zai cafke masu laifin ba, har ma zai fayyace dukkan yanayin da ya kewaye faruwar lamarin.
Ya ce, “Muna jajanta wa Gwamnatin Jihar Borno, mazauna jihar da kuma iyalan da suka rasa ‘yan’uwan su a wannan hari.
“Gwamnatin Tarayya na da yaƙinin cewa waɗanda ke da alhakin wannan abin ƙyama na ta’addanci za su fuskanci cikakken hukuncin doka.”
Ya tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa jajircewar gwamnatin Tinubu wajen kare tsaron ƙasa, bisa tanadin kundin tsarin mulki, ba za ta ja da baya ba.
“Tun bayan da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya hau mulki a shekarar 2023, wannan gwamnati ta ci gaba da jaddada ƙudirin ta na kare tsaro, haɗin kai da kwanciyar hankali na ƙasar mu.
“Wannan ƙudiri na nan daram ƙarƙashin Allah da Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Jamhuriyar Nijeriya.
“Za mu ci gaba da bai wa hukumomin tsaro dukkan albarkatun da tallafin da suke buƙata domin murƙushe ta’addanci a kowane irin salo,” inji shi.







