• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Wasanni

Gwamnatin Tarayya ta taya Super Eagles murna bisa samun lambar tagulla a gasar AFCON

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
January 17, 2026
in Wasanni
A A
0
Gwamnatin Tarayya ta taya Super Eagles murna bisa samun lambar tagulla a gasar AFCON
Super Eagles lokacin gasar AFCON a Marokko

Super Eagles lokacin gasar AFCON a Marokko

Gwamnatin Tarayya ta taya ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Super Eagles murna bisa samun lambar yabo ta tagulla a gasar Kofin Nahiyar Afrika (AFCON) ta 2025, inda ta bayyana rawar da ƙungiyar ta taka a matsayin abin alfahari da farin ciki ga ’yan Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da aka fitar ranar Asabar, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jinjina wa ‘yan ƙungiyar bisa yadda suka ɗaukaka tarihin ƙwallon ƙafa na Nijeriya da zuciya ɗaya, ƙwarewa, da jajircewa a tsawon gasar.

A cewar Ministan, Super Eagles sun nuna jarumta, haɗin kai, da amincewa da juna tun daga matakin rukunoni har zuwa busar ƙarshe a birnin Kasablanca na ƙasar Marokko, wanda hakan ya zaburar da miliyoyin ‘yan Nijeriya a gida da kuma ƙasashen waje.

Ya bayyana cewa irin wasan da suka yi ya wuce kawai buga ƙwallo, domin ya farfaɗo da kishin ƙasa da kuma kyakkyawar fata.

Ministan ya ce samun lambar tagulla ya sake ƙara wa tarihin nasarorin Nijeriya armashi a gasar AFCON, tare da ƙarfafa martabar da Super Eagles ke da ita a nahiyar.

Ya yaba wa ladabi da ruhin gwagwarmaya na ƙungiyar, musamman a wasannin da suka fafata da gaggan ƙungiyoyi.

Haka kuma, ya miƙa godiyar sa ga masu horaswa, ma’aikatan tallafi, da ‘yan wasan bisa sadaukarwa da jajircewar su duk da ƙalubalen da suka fuskanta.

Ya jaddada cewa wasan nasu ya nuna muhimmancin aiki tare, imani, da alfahari wajen wakiltar Nijeriya, ya ƙara da cewa wannan ƙoƙari ya sake tabbatar da matsayin Nijeriya a matsayin babbar ƙasa a ƙwallon ƙafar Afrika.

Ko da yake ya bayyana cewa babban kofin ta suɓuce musu a wannan karo, Ministan ya jaddada cewa an samu lambar tagullar cikin mutunci da ƙoƙari, kuma ba ta ‘yan wasan ba ce kawai, har ma ta ɗaukacin ‘yan Nijeriya ce waɗanda suka ba su goyon baya kuma suka yi imani da su a duk tsawon gasar.

Ya buƙaci Super Eagles da su yi murnar wannan nasara cikin alfahari, tare da ɗaukar ta a matsayin abin ƙarfafa gwiwa domin tunkarar duk wani ƙalubale nan gaba, sannan ya nuna godiya da jinjina kan yadda suka wakilci ƙasar nan.

Tags: AFCONMohammedIdrisSuperEaglestagullaƙwallonƙafa
Previous Post

Tinubu ya yi jimamin rasuwar limamin da ya ceci Kiristoci sama da 200 a Filato

Next Post

Tinubu ya yi tir da kisan gillar da aka yi wa uwa da ‘ya’ya shida a Kano

Related Posts

Ku jaruman gaske ne na ƙasar mu, Uwargidan Shugaban Ƙasa ta faɗa wa ‘yan wasa a taron kammala Gasar Naƙasassu ta Ƙasa karo na 3
Wasanni

Ku jaruman gaske ne na ƙasar mu, Uwargidan Shugaban Ƙasa ta faɗa wa ‘yan wasa a taron kammala Gasar Naƙasassu ta Ƙasa karo na 3

April 3, 2026
CAF ta ƙwace kofin zakarun AFCON na 2025 daga Senegal, ta bai wa Morokko
Wasanni

CAF ta ƙwace kofin zakarun AFCON na 2025 daga Senegal, ta bai wa Morokko

March 17, 2026
AFCON: Gwamnatin Tarayya ta zaburar da Super Eagles gabanin wasan kusa da na ƙarshe da Marokko
Wasanni

AFCON: Gwamnatin Tarayya ta zaburar da Super Eagles gabanin wasan kusa da na ƙarshe da Marokko

January 14, 2026
AFCON 2025: Lookman ya zaburar da Eagles zuwa nasarar 3-2 kan Tunisiya, sun samu tikitin zuwa zagaye na gaba
Wasanni

AFCON 2025: Lookman ya zaburar da Eagles zuwa nasarar 3-2 kan Tunisiya, sun samu tikitin zuwa zagaye na gaba

December 28, 2025
Bankwana da 2025: Shekarar da Harry Kane ya ci ƙwallaye 60 a Bayern, Mbappe ya ci 59 a Madrid
Wasanni

Bankwana da 2025: Shekarar da Harry Kane ya ci ƙwallaye 60 a Bayern, Mbappe ya ci 59 a Madrid

December 23, 2025
Ziyarar Messi a Indiya ta rikiɗe zuwa hargitsi yayin da masoyan sa suka lalata filin wasa saboda ficewar sa ba zato ba tsammani
Wasanni

Ziyarar Messi a Indiya ta rikiɗe zuwa hargitsi yayin da masoyan sa suka lalata filin wasa saboda ficewar sa ba zato ba tsammani

December 14, 2025
Next Post
Tinubu ya yi tir da kisan gillar da aka yi wa uwa da ‘ya’ya shida a Kano

Tinubu ya yi tir da kisan gillar da aka yi wa uwa da 'ya'ya shida a Kano

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!