• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Wasanni

AFCON: Gwamnatin Tarayya ta zaburar da Super Eagles gabanin wasan kusa da na ƙarshe da Marokko

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
January 14, 2026
in Wasanni
A A
0
AFCON: Gwamnatin Tarayya ta zaburar da Super Eagles gabanin wasan kusa da na ƙarshe da Marokko
Ƙungiyar Super Eagles. (Hoto: Akor Adams/X)

Ƙungiyar Super Eagles. (Hoto: Akor Adams/X)

Gwamnatin Tarayya ta nuna cikakken goyon bayan ta ga ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Super Eagles gabanin wasan kusa da na ƙarshe na gasar AFCON da za su fafata da takwarar su ta ƙasar Marokko, inda ta tabbatar wa da ’yan wasan cewa ɗaukacin al’ummar ƙasar nan suna tare da su.

Da ƙarfe 9 na daren yau Laraba ne dai za a fafata tsakanin Nijeriya da Marokko a birnin Rabat.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Laraba, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya buƙaci ’yan wasan ƙasar da su ci gaba da mayar da hankali, sannan su yi amfani da nasarorin da suka samu zuwa yanzu a matsayin makamin tunkarar wasan.

Ministan ya ce: “Ya ku Super Eagles, yayin da kuke shirin fafatawa da Momarokko a wasan kusa da na ƙarshe, ina son ku sani cewa ɗaukacin Nijeriya tana tare da ku. Bajintar da kuka nuna zuwa yanzu abin alfahari ne. Wasa bayan wasa, kuna nuna ƙwazo, juriya, da yaƙini, kuna tunatar da mu dalilin da ya sa Super Eagles take ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da aka fi girmamawa a Afrika.”

Ya tunatar da ’yan wasan irin ɗaukakar da Nijeriya take da ita a fagen ƙwallon ƙafa na nahiyar, inda ya bayyana cewa nasarorin da aka samu a baya sun samo asali ne daga haɗin kai, ƙwarin gwiwa, da jajircewa.

Idris ya ce: “Kun taɓa kaiwa wannan mataki a baya, kuma kun san abubuwan da ake buƙata don samun nasara a mataki irin wannan. Tun daga kofunan AFCON da kuka taɓa ɗagawa zuwa ga manyan ƙungiyoyin da kuka yi nasara a kan su, ko yaushe kuna ɗaga tutar Nijeriya cikin alfahari.

“Waɗannan nasarorin ba haka nan aka same su ba; sakamakon aiki tare ne, da ƙwarin gwiwa, da kuma ruhin fafatawa. Kun nuna wannan ruhi a wannan gasa ma.”

Ministan ya ƙarfafa wa ƙungiyar gwiwa da su shiga fili da ƙwarin gwiwar zakaru, yana mai jaddada cewa miliyoyin ‘yan Nijeriya suna samun ƙwarin gwiwa daga ƙwazon da suke nunawa.

“Yayin da kuka shiga cikin fili, ku sani cewa ba ku kaɗai ba ne. Kuna ɗauke da fatan miliyoyin ‘yan Nijeriya. Sun amince da ku, kuma suna samun ƙwarin gwiwa daga bajintar da kuke nunawa.

“Ku buga wasa da ƙwarin gwiwar zakaru, da haɗin kan ’yan’uwan juna, da kuma kishin cin nasara. Ku tuna tarihin ɗaukakar ku da kuma ƙimar da kuke da ita,” inji shi.

Yayin da yake kira ga nuna tsantsar sadaukarwa, Idris ya buƙaci ’yan wasan da su kasance masu mayar da hankali da jajircewa har zuwa ƙarshen wasan.

“Ku mai da hankali, ku yarda da juna, sannan ku bayar da dukkan ƙarfin ku tun daga farkon wasa har zuwa ƙarshe. Ku ci kowace ƙwallo, ku fafata don samun kowace dama. Kada ku taɓa kokwanto kan abin da za ku iya cimma muddin kuna tare. Kun cancanci kaiwa wannan mataki, kuma kuna da dukkan ƙwarewar da zai kai ku ma fiye da haka,” inji shi.

Daga ƙarshe, ya ƙalubalanci Super Eagles da su sake ba ƙasar alfahari.

“A daren yau, ku fita ku rubuta wani sabon babi na alfahari a tarihin ƙwallon ƙafar Nijeriya. Ku buga da zuciya ɗaya. Ku buga cikin alfahari. Ku buga domin Nijeriya. Allah ya yi muku albarka, Super Eagles. Allah ya albarkaci Tarayyar Jamhuriyar Nijeriya,” inji shi.

Tags: AFCONMarokkoMoroccoNijeriya
Previous Post

Rawar da Babban Bankin Nijeriya ke takawa a tallafin kuɗin noma

Next Post

Gwamnatin Tarayya da ASUU sun ƙulla yarjejeniya ta farko a tarihi domin kawo ƙarshen yawan yajin aiki a jami’o’i

Related Posts

Ku jaruman gaske ne na ƙasar mu, Uwargidan Shugaban Ƙasa ta faɗa wa ‘yan wasa a taron kammala Gasar Naƙasassu ta Ƙasa karo na 3
Wasanni

Ku jaruman gaske ne na ƙasar mu, Uwargidan Shugaban Ƙasa ta faɗa wa ‘yan wasa a taron kammala Gasar Naƙasassu ta Ƙasa karo na 3

April 3, 2026
CAF ta ƙwace kofin zakarun AFCON na 2025 daga Senegal, ta bai wa Morokko
Wasanni

CAF ta ƙwace kofin zakarun AFCON na 2025 daga Senegal, ta bai wa Morokko

March 17, 2026
Gwamnatin Tarayya ta taya Super Eagles murna bisa samun lambar tagulla a gasar AFCON
Wasanni

Gwamnatin Tarayya ta taya Super Eagles murna bisa samun lambar tagulla a gasar AFCON

January 17, 2026
AFCON 2025: Lookman ya zaburar da Eagles zuwa nasarar 3-2 kan Tunisiya, sun samu tikitin zuwa zagaye na gaba
Wasanni

AFCON 2025: Lookman ya zaburar da Eagles zuwa nasarar 3-2 kan Tunisiya, sun samu tikitin zuwa zagaye na gaba

December 28, 2025
Bankwana da 2025: Shekarar da Harry Kane ya ci ƙwallaye 60 a Bayern, Mbappe ya ci 59 a Madrid
Wasanni

Bankwana da 2025: Shekarar da Harry Kane ya ci ƙwallaye 60 a Bayern, Mbappe ya ci 59 a Madrid

December 23, 2025
Ziyarar Messi a Indiya ta rikiɗe zuwa hargitsi yayin da masoyan sa suka lalata filin wasa saboda ficewar sa ba zato ba tsammani
Wasanni

Ziyarar Messi a Indiya ta rikiɗe zuwa hargitsi yayin da masoyan sa suka lalata filin wasa saboda ficewar sa ba zato ba tsammani

December 14, 2025
Next Post
Gwamnatin Tarayya da ASUU sun ƙulla yarjejeniya ta farko a tarihi domin kawo ƙarshen yawan yajin aiki a jami’o’i

Gwamnatin Tarayya da ASUU sun ƙulla yarjejeniya ta farko a tarihi domin kawo ƙarshen yawan yajin aiki a jami’o’i

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!