• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
August 22, 2025
in Labarai
A A
0
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa
Alhaji Mohammed Idris, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai

Alhaji Mohammed Idris, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai

GWAMNATIN Tarayya ta sha alwashin cafke da kuma hukunta masu hannu a kisan da aka yi wa wasu masallata a Ƙaramar Hukumar Malumfashi ta Jihar Katsina.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana wannan hari a matsayin “hari ne na rashin imani da ta’addanci,” tare da jaddada cewa ba zai wuce ba tare da hukunci ba.

Ministan ya ce jami’an tsaro suna kan bin sawun ‘yan ta’addan, tare da tabbatar da cewa “ba za a bar wata kafa ba sai an kama su, kuma an hukunta su yadda ya dace.”

Ya ƙara da cewa: “Gwamnati tana tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa adalci zai kasance cikin gaggawa kuma mai ƙarfi, kuma ba za a taɓa bari irin waɗannan ayyukan ta’addancin su samu gindin zama a ƙasar nan ba.”

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan, al’ummar Malumfashi da kuma Gwamnatin Jihar Katsina.

Idris ya ce: “Damuwa da baƙin cikin su namu ne, kuma gwamnati tana tare da su a wannan lokaci mai duhu. Allah Maɗaukaki ya jiƙan waɗanda suka rasu, ya kuma bai wa waɗanda suka rage ƙarfin zuciya da juriyar ɗaukar wannan babban rashi.”

Ministan ya kuma jaddada nasarorin da ake samu kwanan nan a yaƙi da ta’addanci, inda ya bayyana cewa Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci ta Ƙasa (NCTC) ta cafke manyan shugabannin ƙungiyar ta’addanci ciki har da Mahmud al-Nigeri na ƙungiyar Mahmuda, da mataimakin sa Abu Abba, da kuma Mahmud Muhammad Usman (Abu Bara’a) na ƙungiyar Ansaru – waɗanda dukkan su suna cikin jerin masu laifi da ake nema a duniya.

Ya ce: “Wannan kama manyan shugabannin ya nuna irin nasarorin da ake samu a cikin ayyukan yaƙi da ta’addanci a ƙasar nan, bisa umarnin Shugaban Ƙasa Tinubu, wanda ya bayyana a sarari cewa ayyukan ta’addanci da ke barazana ga Nijeriya da ‘yan ƙasa nan ba da jimawa ba za su zama tarihi.”

Ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya ba za ta taɓa barin wanda ya zubar da jinin jama’a ya samu mafaka a Nijeriya ba.

Previous Post

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Next Post

Tinubu Ya Naɗa Rotimi Pedro Sabon Darakta-Janar na NTA, Kuma Ya Naɗa Manyan Daraktoci Uku Mata

Related Posts

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Next Post

Tinubu Ya Naɗa Rotimi Pedro Sabon Darakta-Janar na NTA, Kuma Ya Naɗa Manyan Daraktoci Uku Mata

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!