• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Tsaro

Gwamnatin Tarayya ta ƙarfafa tsaro a Arewa-ta-Tsakiya bayan harin Kwara – Idris

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
February 13, 2026
in Tsaro
A A
0
Gwamnatin Tarayya ta ƙarfafa tsaro a Arewa-ta-Tsakiya bayan harin Kwara – Idris
Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Gwamnatin Tarayya ta ƙarfafa ayyukan tsaro a yankin Arewa-ta-Tsakiya bayan hare-haren da suka yi sanadin mutuwar kusan mutane 75 a Jihar Kwara.

Idris ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a.

A cewar sa, sabon farmakin tsaron, wanda aka yi wa laƙabi da “Operation Savannah Shield,” ya haɗa da tura dakarun soji, jami’an ’yan sanda da jami’an rundunar tsaron daji na ƙasa domin ƙarfafa tsaro a yankunan da abin ya shafa.

Ya ƙara da cewa manufar matakin shi ne kare fararen hula a al’ummomin da ke fuskantar barazana bayan abin da ya bayyana a matsayin harin ta’addanci na matsorata da aka kai a Jihar Kwara.

Ministan ya ce rundunonin tsaron na samun tallafin fasahar tattara bayanan sirri da kuma tsarin ba-ta-kashi na gaggawa.

Ya bayyana cewa ana gudanar da wannan aiki ne a ƙarƙashin faɗaɗa hurumin tsaro da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya kafa, lokacin da ya ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaron ƙasa a ranar 26 ga Nuwamba, 2026.

A cewar Idris, Shugaban Ƙasar ya yi Allah-wadai da hare-haren na Kwara, inda ya bayyana su a matsayin “na dabbanci, maras tausayi, kuma alamar wata fafutuka ta ’yan ta’adda da ta riga ta gaza, wadda ke kai hari kan fararen hula marasa kariya.”

Ya kuma ba da umurnin cewa “a yi amfani da dukkan ƙarfin gwamnati wajen hukunta duk masu kawo barazana ga zaman lafiya.”

Ministan ya ƙara da cewa tare da ƙara yawan jami’an tsaro a al’ummomin da ke cikin haɗari, Shugaban Ƙasa ya nuna ƙudirin gwamnatin sa na kare rayukan ’yan Nijeriya da kuma tabbatar da ’yancin su na yin addini cikin walwala.

Haka kuma, a cewar sa, an ƙarfafa tsaro a wuraren ibada, ciki har da ƙara yawan jami’an tsaro a kewayen majami’u a ranakun Lahadi, tare da haɗin gwiwa da shugabannin al’umma da na addini.

A wani ɓangare na ƙarfafa tsarin tsaro gaba ɗaya, Ministan ya ce Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya ta janye jami’an ta da ke raka manyan mutane zuwa ayyukan sintiri da tsaron al’umma a faɗin ƙasar nan.

Idris ya ce wannan matakin ya haifar da ƙarin tsaro a jihohin Kwara, Filato, Binuwai, Kogi, Nasarawa, Neja, da kuma Gundumar Babban Birnin Tarayya (FCT).

Haka nan, ya ce Shugaba Tinubu ya sha jaddada cewa yaƙin da Nijeriya take yi da ta’addanci zai ci gaba da kasancewa ƙarƙashin jagorancin Nijeriya, ko da yake ana maraba da haɗin gwiwa daga abokan hulɗa na ƙasashen duniya idan buƙatar hakan ta taso.

Ya ce: “Yaƙin da Nijeriya take yi da ta’addanci zai ci gaba da kasancewa ƙarƙashin jagorancin Nijeriya kuma bisa ikon ta. Inda ya dace kuma ya yi daidai da muradun ƙasa, gwamnati tana maraba da haɗin gwiwa mai faɗi, ciki har da daga Amurka da sauran abokan hulɗa ta fannin tattara bayanan sirri da sa ido, domin tallafa wa manufofin da Nijeriya ta tsara, kuma domin amfanin ’yan Nijeriya.”

Tags: MohammedIdrista'addancitsaro
Previous Post

Sarkin Adabi: Mafi Girman Sarautar Fasaha

Next Post

Mun samu damar sauraron kiran wayar Ribaɗu, mun ji yadda ya ba da umurnin a kama ni, inji El-Rufai

Related Posts

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma
Tsaro

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma

April 25, 2026
Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos
Tsaro

Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos

April 17, 2026
‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya
Tsaro

‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya

April 16, 2026
Sojoji sun ragargaji maɓoyar ‘yan ta’adda a dajin Bauchi, sun kamo iyalan su
Tsaro

Sojoji sun ragargaji maɓoyar ‘yan ta’adda a dajin Bauchi, sun kamo iyalan su

April 15, 2026
Nijeriya ba za ta miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba – Gwamnatin Tarayya
Tsaro

Gwamnatin Tarayya ta kare harin jirgin sama a Jilli, ta ba da umurnin bincike

April 14, 2026
An kashe kwamanda da sojoji shida ta hanyar bam a Borno
Tsaro

An kashe kwamanda da sojoji shida ta hanyar bam a Borno

April 13, 2026
Next Post
Mun samu damar sauraron kiran wayar Ribaɗu, mun ji yadda ya ba da umurnin a kama ni, inji El-Rufai

Mun samu damar sauraron kiran wayar Ribaɗu, mun ji yadda ya ba da umurnin a kama ni, inji El-Rufai

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!