• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Tsaro

Gwamnatin Tarayya da Amurka za su haɗa kai don inganta ’yancin addini da ƙarfafa tsaro a Nijeriya

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
January 23, 2026
in Tsaro
A A
0
Gwamnatin Tarayya da Amurka za su haɗa kai don inganta ’yancin addini da ƙarfafa tsaro a Nijeriya
Mashawarci ga Shugaban Ƙasa kan Tsaron Ƙasa, Malam Nuhu Ribaɗu, da Ƙaramar Sakataren Harkokin Waje ta Amurka, Allison Hooker, a taron

Mashawarci ga Shugaban Ƙasa kan Tsaron Ƙasa, Malam Nuhu Ribaɗu, da Ƙaramar Sakataren Harkokin Waje ta Amurka, Allison Hooker, a taron

Gwamnatocin Tarayya da ta Amurka sun cimma matsaya kan cewa daga yanzu za su haɗa gwiwa don inganta ’yancin yin addini tare da ƙarfafa tsaro a duk faɗin Nijeriya.

Yarjejeniyar ta biyo bayan taron farko na Guruf ɗin Aikin Haɗin Gwiwa na Amurka da Nijeriya wanda aka gudanar a Abuja a ranar Alhamis, 22 ga Janairu, 2026.

An kafa wannan Guruf ɗin Aiki ne sakamakon sanya Nijeriya a matsayin Ƙasa Mai Bada Matukar Damuwa (wato “Country of Particular Concern“) da Shugaban Amurka Donald J. Trump ya yi a ƙarƙashin Dokar ’Yancin Yin Addini ta Ƙasa da Ƙasa (International Religious Freedom Act).

Ta hanyar haɗin gwiwa ta ƙut-da-ƙut, manufofin Guruf ɗin Aikin su ne rage tashin hankali da ake yi wa ƙungiyoyi masu rauni a Nijeriya, musamman Kiristoci, da kuma samar da yanayi mai kyau da zai ba dukkan ’yan Nijeriya damar yin addinin su cikin ’yanci ba tare da cikas daga ’yan ta’adda, ’yan a-ware, ’yan fashi da makami, da ƙungiyoyin ’yan bindiga ba, ko kuma duk waɗanda ke son cutar da fararen hula ba tare da la’akari da addinin su ba.

A taron na Abuja, Mashawarci ga Shugaban Ƙasa kan Tsaron Ƙasa, Malam Nuhu Ribaɗu, shi ne ya jagoranci tawagar Nijeriya wadda ta ƙunshi Ma’aikatun Gwamnati da hukumomi guda 10, yayin da Ƙaramar Sakataren Harkokin Waje ta Amurka, Allison Hooker, ta jagoranci tawagar Amurka wadda ta ƙunshi hukumomin tarayyar ƙasar guda takwas.

A takardar bayan taron wadda aka raba wa manema labarai a ranar Alhamis, an bayyana cewa tattaunawar dabaru a zaman da aka yi sun mayar da hankali ne kan fannoni da dama na batutuwa da ƙalubale inda haɗin gwiwar Amurka da Nijeriya zai inganta ’yancin yin addini tare da ƙarfafa tsaro a faɗin ƙasar nan.

Ɓangarorin biyu sun yi la’akari da cewa akwai fa daɗaɗɗiyar alaƙa a tsakanin ƙasashen biyu, wadda ta ginu bisa ƙimomin haɗin kai na al’ummomi masu bambancin ra’ayi, girmama doka da oda, da mutunta ikon ƙasa.

Ɓangaren Amurka sun yi maraba da bayanin sake daidaita albarkatun Nijeriya domin magance rashin tsaro, musamman a jihohin Arewa-ta-Tsakiya. Gwamnatocin biyu sun sake jaddada ƙudiri mai ƙarfi da ba ya sassauci na kare ƙa’idojin ’yancin yin addini, tare da buƙatar ɗaukar matakai na haɗin gwiwa, masu ɗorewa da aiki tuƙuru, domin haɓakawa da kare ’yancin faɗar albarkacin baki, taron lumana, da ’yancin addini ko aƙida ga kowa, daidai da Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Nijeriya.

Mahartan taron sun kuma jaddada muhimmancin kare jama’a farar hula, musamman al’ummar Kirista masu rauni, da kuma ɗaukar matakin hukunta masu aikata tashin hankali.

Ɓangarorin biyu sun sake tabbatar da aniyar su ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwar yaƙi da ta’addanci, ciki har da aiki tare ta fannin ayyukan haɗin gwiwa na aiki, samun damar amfani da fasaha, yaƙi da safarar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba, hana tallafa wa ta’addanci da kuɗi, da gina ƙarfin hukumomin tsaro da bincike.

Tawagar Amurka ta gode wa Nijeriya bisa matakan gaggawa da ta ɗauka na ƙarfafa tsaro ga al’ummar Kiristoci da ke cikin haɗari, da kuma ’yan Nijeriya na dukkan addinai da rayuwar su take fuskantar barazana sakamakon tashin hankali da ta’addanci.

An yanke shawarar cewa za a gudanar da taro na gaba na Guruf ɗin Aikin a Amurka, a wata ranar da ta dace da ɓangarorin biyu, wadda za a tsara ta hanyar hanyoyin diflomasiyya.

Tags: addiniAllisonHookerAmurkaNuhuRibaduShugabaDonaldTrumptarotsaroyarjejeniya
Previous Post

Satar mutane a Kaduna: Amurka ta buƙaci Nijeriya ta ƙara kariya ga Kiristoci

Next Post

CBN zai fito da tsarin magance yawan samun matsalolin kati da na’urar ATM

Related Posts

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma
Tsaro

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma

April 25, 2026
Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos
Tsaro

Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos

April 17, 2026
‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya
Tsaro

‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya

April 16, 2026
Sojoji sun ragargaji maɓoyar ‘yan ta’adda a dajin Bauchi, sun kamo iyalan su
Tsaro

Sojoji sun ragargaji maɓoyar ‘yan ta’adda a dajin Bauchi, sun kamo iyalan su

April 15, 2026
Nijeriya ba za ta miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba – Gwamnatin Tarayya
Tsaro

Gwamnatin Tarayya ta kare harin jirgin sama a Jilli, ta ba da umurnin bincike

April 14, 2026
An kashe kwamanda da sojoji shida ta hanyar bam a Borno
Tsaro

An kashe kwamanda da sojoji shida ta hanyar bam a Borno

April 13, 2026
Next Post
CBN zai fito da tsarin magance yawan samun matsalolin kati da na’urar ATM

CBN zai fito da tsarin magance yawan samun matsalolin kati da na'urar ATM

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!