• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Ƙasashen Duniya

Chana ta gargaɗi Amurka da ta daina tsoma baki a ƙasashen waje kan zargin tauye ‘yancin addini

Wakilin Mu by Wakilin Mu
November 4, 2025
in Ƙasashen Duniya
A A
0
Chana ta gargaɗi Amurka da ta daina tsoma baki a ƙasashen waje kan zargin tauye ‘yancin addini
Miss Mao Ning

Miss Mao Ning

Gwamnatin ƙasar Chana ta bayyana cikakken goyon bayan ta ga Nijeriya a daidai lokacin da ake samun zazzafar muhawara kan sukar da Amurka ta yi kan yadda gwamnatin Nijeriya ke tafiyar da batutuwan addini a cikin ƙasar nan.

Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Waje ta China, Madam Mao Ning, ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da aka wallafa a shafin ma’aikatar a yau Talata, inda ta ce ƙasar ta tana adawa da duk wani ƙoƙarin tsoma baki cikin harkokin cikin gida na kowace ƙasa, musamman da sunan kare ‘yancin addini ko ɗan’adam.

Ta ce: “A matsayin ta na abokiyar hulɗa ta dabarun cigaba da Nijeriya, Chana na cikakken goyon bayan gwamnatin Nijeriya wajen jagorantar al’ummar ta bisa tsarin da ya dace da halin da ƙasar take ciki.

“Muna adawa da duk wata ƙasa da ke tsoma baki cikin harkokin wasu ƙasashe da sunan addini ko kare ‘yancin ɗan’adam. Muna kuma adawa da barazanar sanya takunkumi ko amfani da ƙarfi don tilasta wa wata ƙasa bin wata hanya.”

Wannan matsayi na Chana yana zuwa ne bayan Shugaba Donald Trump ya bayyana Nijeriya a matsayin “ƙasa mai matsala ta musamman” saboda, a cewar sa, ana zaluntar mabiya addinin Kirista a ƙasar.

Trump ya yi barazanar cewa Amurka na iya dakatar da duk wani taimako ga Nijeriya, ko ma ta ɗauki matakin soja idan gwamnatin Nijeriya “ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci.”

Masana harkokin diflomasiyya sun bayyana cewa kalaman Trump na iya dagula dangantaka tsakanin Amurka da Nijeriya, musamman ganin yadda Chana ke ƙara ƙarfafa hulɗar tattalin arziki da diflomasiyya da Nijeriya a ƙarƙashin tsarin BRICS.

Chana ta kasance ɗaya daga cikin manyan abokan hulɗar tattalin arziki na Nijeriya, tana zuba jari a fannoni da dama kamar makamashi, gine-gine da fasahar zamani, tare da nuna goyon bayan siyasa da diflomasiyya ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Tags: AmurkaChanadiflomasiyyaDonald TrumpMao NingShugaba Bola Ahmed Tinubu
Previous Post

Shirin ƙarfafa jari: CBN ya shawarci bankuna marasa ƙarfi su haɗe ko su rage wa lasisin su geji

Next Post

Yadda Tinubu ya magance tsadar abinci ba tare da samun cikas ga Shirin Farfaɗo da Noma a Nijeriya ba

Related Posts

Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce
Ƙasashen Duniya

Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce

April 24, 2026
Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma
Ƙasashen Duniya

Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma

April 20, 2026
Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa
Ƙasashen Duniya

Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa

April 20, 2026
Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran
Ƙasashen Duniya

Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran

April 18, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Ƙasashen Duniya

CBN na shirin kafa kwamitin sulhu don warware rikice-rikicen masu taurin bashi

April 17, 2026
Iran ta kakkaɓo jirgin yaƙin Amurka a sararin samaniyar ta
Ƙasashen Duniya

Iran ta kakkaɓo jirgin yaƙin Amurka a sararin samaniyar ta

April 3, 2026
Next Post
Tsaro: Tinubu ya kira taron Majalisar Ƙoli ta ƙasa da ta ‘yan sanda

Yadda Tinubu ya magance tsadar abinci ba tare da samun cikas ga Shirin Farfaɗo da Noma a Nijeriya ba

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!