Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa sama da kashi 97 na ‘yan Nijeriya ba za su biya haraji ba kwata-kwata.
Shugaban kwamitin gyaran haraji, Mista Taiwo Oyedele, shi ne ya faɗi hakan a wata hira da aka yi da shi a tashar talbijin ta Channels inda ya lissafa jerin waɗanda biyan sabon tsarin haraji da gwamnati ta fito da shi ba zai shafe su ba.
Ya lissafa su kamar haka:
1. Masu karɓar mafi ƙarancin albashi na N70,000 zuwa ƙasa.
2. Waɗanda kuɗin shigar su bai zarce N100,000 ba a wata.
3. ‘Yan kasuwa masu jarin ƙasa da naira miliyan biyu.
4. Kamfanoni da a da ake karɓar haraji a hannun su duk da kadarar su ba ta haura naira miliyan 25 ba, yanzu sai kadarar su ta kai naira miliyan 100 sannan za su biya haraji.
6. Waɗanda ke biyan tarin haraje-haraje ma ba a bar su a baya ba, domin daga shekarar 2026 za su fara biyan haraji ɗaya tal, kuma mafi ƙaranci.
Shugaban ya kuma bayyana yadda mutum zai gane cewa bai cancanci biyan haraji ba, ya ce tuni suka tanadi hatimi a manhajar QR kan shafin yanar gizo na tsarin harajin, inda duk mai buƙatar sanin matsayin sa zai je ya ɗauki hoton hatimin QR ɗin ya zura sunan sa da bayanin kuɗaɗen shigar sa don sanin ya dace ya biya haraji ko a’a.







