• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

ACF ta dakatar da shugaban kwamitin amintattu, Bashir Ɗalhatu bisa zargin rashin gaskiya

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
May 6, 2026
in Labarai
A A
0
ACF ta dakatar da shugaban kwamitin amintattu, Bashir Ɗalhatu bisa zargin rashin gaskiya
Malam Murtala Aliyu (a hagu) da Alhaji Bashir Ɗalhatu

Malam Murtala Aliyu (a hagu) da Alhaji Bashir Ɗalhatu

Kwamitin zartarwa na ƙasa na Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (Arewa Consultative Forum, ACF) ya dakatar da shugaban kwamitin amintattu (BoT) na ƙungiyar, Alhaji Bashir Ɗalhatu (Wazirin Dutse), bisa zargin rashin gaskiya wajen harkokin kuɗi da kuma karya kundin tsarin mulki.

NEC ta dakatar da Ɗalhatu ne a yau Laraba yayin wani taron gaggawa da aka gudanar a Kaduna, wanda wakilai daga jihohin arewa 18 da Babban Birnin Tarayya (FCT) suka halarta.

Da yake magana da manema labarai bayan taron, kakakin ACF, Tukur Muhammad Baba, ya ce an sauya wurin taron NEC ne bayan da ‘yan sanda suka rufe sakatariyar ƙungiyar da ke Titin Sokoto.

Sai dai kakakin ‘yan sanda na Kaduna, Mansir Hassan, ya ce an rufe sakatariyar ne domin hana yiwuwar rikicewar doka da oda.

Rikicin da ke cikin ƙungiyar ya biyo bayan saɓani kan wa’adin mulkin wasu jami’ai.

Matsalar ta fara ne lokacin da Ɗalhatu ya nuna damuwa kan ƙarewar wa’adin wasu masu riƙe da muƙamai, ciki har da Babban Sakataren ACF, Alhaji Murtala Aliyu (Matawallen Gombe).

A cikin wata sanarwa da ya fitar, Ɗalhatu ya ambaci tanade-tanaden kundin tsarin mulkin ACF, wanda ya tanadi wa’adi guda ɗaya na shekaru shida ga membobin BoT, yayin da membobin NEC ke da wa’adin shekaru uku wanda za a iya sabunta shi sau ɗaya.

Ya ƙara da cewa BoT ta riga ta karɓi wata takarda daga “membobi da abin ya dama” wadda ke zargin karya kundin tsarin mulki.

Ɗalhatu ya ce an tattauna batun a wani taron BoT da aka gudanar ranar 23 ga Afrilu, 2026, inda aka yanke hukuncin cewa wa’adin jami’an da suka fara aiki a watan Maris na 2020 ya ƙare a ranar 10 ga Maris, 2026.

Ya lissafa waɗanda abin ya shafa da suka haɗa da F. Orti, Mataimakin Shugaban BoT, Ibrahim Sule, Mataimakin Shugaban BoT, Ibrahim Ida, Mataimakin Shugaban NEC, da Murtala Aliyu, Babban Sakatare.

A cewar Ɗalhatu, an tsawaita wa’adin Aliyu zuwa ranar 15 ga Mayu, 2026, domin ba da damar miƙa mulki cikin sauƙi, amma ya ƙi sauka daga muƙamin sa.

Ya bayyana cewa Murtala Aliyu ne kaɗai daga cikin jami’an da abin ya shafa ya ƙi amincewa da matakin.

“A wani yanayi mai ɗaure kai, Malam Murtala Aliyu, wanda yanzu yake shekarar sa ta bakwai a matsayin Babban Sakatare, ya ƙi amincewa da hukuncin kuma yana ci gaba da riƙe da muƙami,” inji Ɗalhatu.

Ya kuma ce an yi ƙoƙarin sasanta rikicin cikin lumana, ciki har da wani taron dattawa da Haliru Aƙilu da Mahmud Ahmed suka shirya ranar 21 ga Afrilu, 2026.

Ɗalhatu ya kuma zargi Aliyu da ƙara rura wutar rikicin ta hanyar kiran taron gaggawa na NEC a ranar 6 ga Mayu domin soke hukuncin BoT.

Duk da zarge-zargen da ake yi masa, Ɗalhatu ya musanta zargin karkatar da kuɗaɗe, yana mai cewa an gudanar da kuɗaɗen asusun tallafin ACF cikin gaskiya da bayyana gaskiya.

Da yake mayar da martani ga zargin, Malam Murtala Aliyu, wanda tsohon Ƙaramin Ministan Wutar Lantarki da Ƙarafa ne, ya ce har yanzu wa’adin sa yana nan daram, yana mai dogaro da bin ƙa’ida da kuma takardun sake naɗa shi.

Ya ce: “An naɗa ni a matsayin Sakatare a watan Maris na 2020, aka rantsar da ni a watan Agusta na 2020, aka sake zaɓe na a watan Yuli na 2023, sannan aka sake rantsar da ni a watan Disamba na 2023. Ina da takardun da ke tabbatar da duk waɗannan.”

Ya ƙara da cewa sake zaɓen sa a shekarar 2023 ya sabunta wa’adin sa, wanda ya sa zargin cewa wa’adin sa ya ƙare bai dace ba.

Tags: ACFArewaBashir ƊalhatudattawaMurtala Aliyurikicin ƙungiyazargi
Previous Post

ICPC ta ƙalubalanci sabuwar buƙatar beli da El-Rufai ya gabatar yayin da kotu ta ɗage sauraron ƙarar zuwa 13 ga Mayu

Next Post

Yadda ƙarfin laƙani da dafa’in CBN ke hana girgizar tattalin arzikin duniya yi wa Nijeriya barazana

Related Posts

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Next Post
Manyan nasarorin da CBN ya samu cikin 2025

Yadda ƙarfin laƙani da dafa'in CBN ke hana girgizar tattalin arzikin duniya yi wa Nijeriya barazana

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!