Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin Dakta Fatima Suleiman Zuntu a matsayin sabuwar Shugaba kuma Babbar Jami’ar Gudanarwa (DG/CEO) ta Hukumar Kula da Ƙwayoyin Halittu ta Ƙasa (NBMA).
Labarin wannan naɗin yana ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da fadar Shugaban Ƙasa ta fitar, inda aka bayyana cewa naɗin nata zai kwashe tsawon shekaru huɗu ne a karo na farko.
An bayyana cewa naɗin ya fara aiki ne tun daga ranar 16 ga Afrilu, 2026, kamar yadda sashi na 5 na dokar hukumar NBMA ta shekarar 2015 ya tanada.
Dakta Fatima Suleiman Zuntu ƙwararriya ce a fannin lafiyar al’umma (Public Health) sannan kuma masaniya ce kan dabarun tsara manufofi.
Kafin naɗin nata, tana da gogewa wajen tafiyar da muhimman shirye-shiryen raya ƙasa waɗanda suka haifar da sakamako mai kyau a matakin ƙasa.
Shugaban Ƙasa ya buƙaci sabuwar shugabar da ta yi amfani da ɗimbin ilimin ta da ƙwarewar ta domin ciyar da hukumar gaba, tare da tabbatar da cewa ayyukan ta sun taimaka wajen kare lafiyar ‘yan ƙasa da muhallin Nijeriya.
Hukumar NBMA dai ita ce ke da alhakin sa ido da kuma tabbatar da cewa duk wani abu da ya shafi ƙwayoyin halittu (GMOs) bai cutar da lafiyar mutane ko ƙasa ba.







