• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Kiwon Lafiya

Uwargidan Shugaban Ƙasa ta ƙaddamar da Asusun Ciyarwar Abinci na Ƙasa, ta ba da gudunmawar naira miliyan 500

* Ta yaba wa Minista Ali Pate kan gyaran harkar lafiya

ALI KANO by ALI KANO
April 3, 2026
in Kiwon Lafiya
A A
0
Uwargidan Shugaban Ƙasa ta ƙaddamar da Asusun Ciyarwar Abinci na Ƙasa, ta ba da gudunmawar naira miliyan 500
Uwargidan Shugaban Ƙasa Oluremi Tinubu tana gabatar da jawabi a taron

Uwargidan Shugaban Ƙasa Oluremi Tinubu tana gabatar da jawabi a taron

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta bayar da gudunmawar Naira miliyan 500 ga sabon Asusun Ciyarwar Abinci na Al’umma da aka ƙaddamar.

An ƙaddamar da wannan asusu ne tare da haɗin gwiwar ofishin Uwargidan Shugaban Ƙasa, Ma’aikatar Lafiya da Jin Daɗin Jama’a ta Tarayya, Hukumar Kula da Cigaban Kiwon Lafiya ta Matakin Farko ta Ƙasa, da Bankin Manoma (BOA), domin gina ingantaccen tsarin rumbun abinci a Nijeriya wanda zai kasance a ƙarƙashin asusun mai tsari, mai tsare gaskiya, kuma mai iya kaiwa ga al’umma da gidaje a faɗin ƙasar nan.

Uwargidan Shugaban Ƙasar ta bayyana wannan tallafi ne yayin ƙaddamar da shirin da kuma rantsar da kwamitin amintattu a wani taro da aka gudanar a ranar Alhamis a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

A jawabin da ta gabatar, Madam Tinubu ta nuna farin ciki kan yadda aka nuna karamci da goyon baya wajen ƙarfafa tsarin tallafin abinci ga gidaje marasa galihu a faɗin Nijeriya.

Ta jaddada buƙatar magance matsalar rashin abinci mai gina jiki mai tsanani a ƙasar nan, inda ta bayyana cewa rashin abinci mai gina jiki ga yara har yanzu babbar matsala ce ta ƙasa, tare da miliyoyin yara da ke buƙatar samun abinci mai gina jiki a kai a kai domin ingantaccen girma da cigaba.

Ta yi gargaɗi cewa, “Rashin ɗaukar mataki yana shafar lafiyar su, girman su, baiwar su da makomar su, don haka magance wannan matsala abu ne mai buƙatar gaggawa kuma muhimmi domin tabbatar da makomar ƙasa.”

Sanata Oluremi Tinubu tare da membobin Kwamitin Amintattu na Asusun Ciyarwar da kuma matan gwamnoni a bayan su.

Ta ƙara da cewa an tsara shirin Rumbun Abinci na Al’umma a matsayin mafita mai ɗorewa domin kawo abinci mai lafiya da gina jiki cikin sauƙi ga yara masu rauni ‘yan ƙasa da shekaru 16, tare da ƙarfafa tsarin abinci a matakin al’umma da dawo da daidaito a rabon abinci.

Ta ce, “Wannan shiri yana daidai da manufar mai girma Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, na inganta tsaron abinci da kare jin daɗin yara ‘yan ƙasa.”

Uwargidan Shugaban Ƙasar ta ƙara da cewa a duniya baki ɗaya, rumbunan abinci sun nuna inganci wajen tabbatar da cewa abinci mai gina jiki ya kai ga waɗanda suka fi buƙata, ta hanyar haɗin gwiwa da manoma, masu sarrafa abinci, kamfanoni, ƙungiyoyin farar hula da cibiyoyin al’umma.

Ta yaba wa masu ruwa da tsaki irin su manyan ‘yan kasuwa, shugabannin kamfanoni, manyan jami’an gwamnati, abokan hulɗar cigaba, sarakuna da shugabannin addini, da ƙungiyoyin farar hula bisa goyon bayan da suka bayar.

Ta kuma bayyana cewa membobin kwamitin amintattun mutane ne masu ƙwarewa, tsare gaskiya da jajircewa a hidimar jama’a.

Madam Tinubu ta bayyana amannar ta cewa za su samar da jagoranci da kulawar da ake buƙata domin gudanar da asusun cikin gaskiya, inganci da riƙon amana, tare da tabbatar da cewa kowane yanki a Nijeriya ya amfana yadda ya dace.

Ta ce: “Ina taya ku murna kuma ina gode maku da karɓar wannan muhimmin nauyi na ƙasa.

“Haka kuma ina yaba wa mutane da ƙungiyoyi da suka nuna amincewa da wannan shiri ta hanyar alƙawurra da gudunmawar da suka bayar.”

Ta yi kira ga sauran ‘yan Nijeriya masu kishin ƙasa, ƙungiyoyi da cibiyoyi da su shiga wannan yunƙuri na ƙasa, inda aka tsara kai shirin zuwa dukkan yankunan siyasa guda shida na ƙasar nan.

Ta kuma yaba wa Ministan Lafiya da Jin Daɗin Jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate, da tawagar sa, da kuma Manajan Darakta kuma Shugaban Bankin Masana’antu, Dakta Olasupo Olusi, bisa haɗin gwiwa da goyon baya da suke bayarwa.

Tun da farko, Farfesa Pate ya bayyana cewa wannan shiri ya zo a wani lokaci mai muhimmanci a tarihin ƙasar nan ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda manufofin sa suka mayar da hankali kan inganta walwala, lafiya da kariyar zamantakewar ‘yan Nijeriya.

Ya kuma yaba da jagorancin Uwargidan Shugaban Ƙasa wajen ƙirƙira da jagorantar shirin, wanda ya dace da hangen nesa na Shugaban Ƙasa ga ɓangaren lafiya.

Ministan ya ƙara da cewa ma’aikatar sa tana aiwatar da gyare-gyare domin ƙarfafa tsarin lafiya ta fannoni daban-daban, yana mai jaddada cewa an faɗaɗa samun kulawar lafiya ta matakin farko domin inganta lafiyar al’umma.

Ya bayyana cewa wasu abokan Uwargidan Shugaban Ƙasa da suka buƙaci a ɓoye sunayen su sun bayar da gudunmawar dala $500,000, yayin da Gwamnatin Tarayya ta bayar da Naira biliyan 17 ta hannun Asusun Tallafin Zamantakewa ga Shirin Rumbun Abinci na Al’umma na Ƙasa.

A wajen taron, an gabatar da saƙonnin fatan alheri da gudunmawa, inda Gidauniyar Ɗangote ta bayar da Naira biliyan 20, sai kamfanin NNPC Ltd. da ya bayar da Naira biliyan 10, yayin da Gidauniyar Emeka ta bayar da Naira miliyan 500 da za a raba cikin shekaru biyar na shirin.

A cikin wata sanarwa ga manema labarai, Mataimakin Darakta na Sashen Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, Ado Bako, ya bayyana cewa an ƙaddamar da shirin Rumbun Abinci na Al’umma na Ƙasa ne domin rage matsalar rashin abinci mai gina jiki a tsakanin masu rauni a al’umma.

Ya ƙara da cewa za a fara aiwatar da shirin a yankuna shida na ƙasar nan daga Afrilu zuwa Yuni 2026, sannan a faɗaɗa shi zuwa dukkan ƙananan hukumomi 774 daga Yuli zuwa Disamba 2026.

Tags: abinciFarfesa Muhammad Ali PateMa'aikatar Kiwon LafiyaRemi Tinubu
Previous Post

Za mu ci gaba da gudanar da babban taron mu, ADC ta ƙalubalanci shugaban INEC

Next Post

Ku jaruman gaske ne na ƙasar mu, Uwargidan Shugaban Ƙasa ta faɗa wa ‘yan wasa a taron kammala Gasar Naƙasassu ta Ƙasa karo na 3

Related Posts

Tinubu ya naɗa Fatima Zuntu shugabar hukumar NBMA
Kiwon Lafiya

Tinubu ya naɗa Fatima Zuntu shugabar hukumar NBMA

April 20, 2026
Likitoci za su fara yajin aiki na gama-gari daga Talata
Kiwon Lafiya

Likitoci za su fara yajin aiki na gama-gari daga Talata

April 5, 2026
Ranar Ji ta Duniya 2026: Dalilan da za a iya kauce wa suna ci gaba da haddasa naƙasar ji a tsakanin yara a Nijeriya – Minista
Kiwon Lafiya

Ranar Ji ta Duniya 2026: Dalilan da za a iya kauce wa suna ci gaba da haddasa naƙasar ji a tsakanin yara a Nijeriya – Minista

March 3, 2026
Nijeriya ta rattaba hannu kan babbar yarjejeniyar zuba jari a fannin kiwon lafiya
Kiwon Lafiya

Nijeriya ta rattaba hannu kan babbar yarjejeniyar zuba jari a fannin kiwon lafiya

February 5, 2026
Amurka za ta kashe dala miliyan 200 na tallafi kai-tsaye ga fiye da asibitoci 900 na mabiya addinin Kirista a Nijeriya
Kiwon Lafiya

Amurka za ta kashe dala miliyan 200 na tallafi kai-tsaye ga fiye da asibitoci 900 na mabiya addinin Kirista a Nijeriya

December 21, 2025
Cewar Minista: Gwamnati ta saki da naira biliyan 32.9 don inganta kiwon lafiya
Kiwon Lafiya

Cewar Minista: Gwamnati ta saki da naira biliyan 32.9 don inganta kiwon lafiya

October 14, 2025
Next Post
Ku jaruman gaske ne na ƙasar mu, Uwargidan Shugaban Ƙasa ta faɗa wa ‘yan wasa a taron kammala Gasar Naƙasassu ta Ƙasa karo na 3

Ku jaruman gaske ne na ƙasar mu, Uwargidan Shugaban Ƙasa ta faɗa wa ‘yan wasa a taron kammala Gasar Naƙasassu ta Ƙasa karo na 3

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!