Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya aika da sunan Alhaji Murtala Sule Garo zuwa Majalisar Dokokin Jihar domin tantancewa da tabbatar da shi a matsayin Mataimakin Gwamna.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yaɗa Labarai na gwamnan, Mustapha Muhammad, ya sanya wa hannu.
Naɗin ya yi daidai da Sashe na 191(3) na Kundin Tsarin Mulki na 1999 (da aka yi wa kwaskwarima), wanda ya bai wa gwamna ikon naɗa mataimakin gwamna idan gurbi ya samu.
Matsayin ya zama babu kowa a ciki ne bayan murabus na ƙashin kan sa da tsohon Mataimakin Gwamna, Kwamared Abdussalam Gwarzo, ya yi a ranar 27 ga Maris.
Bayan tattaunawa sosai da ya yi da masu ruwa da tsaki, gwamnan ya buƙaci Majalisar ta ba da amincewar da ake buƙata domin tabbatar da naɗin Garo.
Garo, wanda ɗan shekara 48 ne, gogaggen ɗan siyasa ne wanda ya kwashe sama da shekaru ashirin yana harkar siyasa inda ya riƙe muƙami da aka zaɓe shi ko na naɗi.
Ya taɓa zama Sakataren Tsare-tsare na Jiha na jam’iyyar sa, Mai Bai wa Gwamnan Jihar Kano Shawara ta Musamman, sannan aka zaɓe shi Shugaban Ƙaramar Hukumar Kabo.
Haka kuma ya taɓa zama Shugaban ƙungiyar ALGON ta Kano, Kwamishinan Ƙananan Hukumomi da Harkokin Masarautu, sannan ya kasance ɗan takarar Mataimakin Gwamna na jam’iyyar APC a babban zaɓen 2023.







