• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Cika Shekaru 25: Ministan Yaɗa Labarai ya jinjina wa tasirin ƙungiyar ActionAid cikin al’umma 

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
November 28, 2025
in Labarai
A A
0
Cika Shekaru 25: Ministan Yaɗa Labarai ya jinjina wa tasirin ƙungiyar ActionAid cikin al’umma 
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Alhaji Mohammed Idris, yana jawabi a taron cikar ƙungiyar ActionAid Nigeria shekaru 25 a ranar Alhamis a Abuja

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Alhaji Mohammed Idris, yana jawabi a taron cikar ƙungiyar ActionAid Nigeria shekaru 25 a ranar Alhamis a Abuja

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Alhaji Mohammed Idris, ya yaba wa ƙungiyar nan mai zaman kan ta ta ActionAid Nigeria bisa cika shekaru 25 da ta yi tana aiki, hidima, da ayyukan sauyi a faɗin ƙasar nan.

Da yake jawabi a bikin cika shekaru 25 da kafuwar ƙungiyar a Abuja a ranar Alhamis, Ministan ya ce, “An samu tsawon rabin ƙarni, ActionAid ta kai ci gaba zuwa matakin farko, tana ba mata da ‘yan mata ƙarfi, tana ƙarfafa ilimi, inganta kiwon lafiya, yin rajin gyaran shugabanci, tallafa wa al’umma a lokutan rikice-rikice, da kuma ƙara wa muryar masu rauni ƙarfi.”

Ya ƙara da cewa ya kamata a yaba wa ActionAid bisa yawan martanin da ta ba mawuyacin halin jinƙai da kuma ayyukan ƙara wa al’umma ƙarfi daga tushe—waɗanda suka sauya manufofi da cigaban al’umma ta hanyoyi masu zurfi da auna tasirin su a Nijeriya.

Ya ce: “A yau, mun taru ne don girmama wannan gado tare da duban babi na gaba.”

Taron cikar ƙungiyar ActionAid Nigeria shekaru 25

Ya jaddada muhimmancin manyan abubuwa guda biyu da aka gabatar a bikin: ƙaddamar da littafin “AAN@25 Legacy Book” da kuma bayyana sabon tsari na ginin ActionAid, yana bayyana su a matsayin alamar bunƙasar ƙungiyar da yaruwar ta a tsawon lokaci a Nijeriya.

Idris ya ce: “Ina kuma farin cikin bayyana tsarin ginin ActionAid, wata alama mai ƙarfi ta bunƙasar ƙungiyar da ɗorewar ta na dogon lokaci a Nijeriya. Wannan jarin da ke kallon gaba yana nuna jajircewar ActionAid wajen zurfafa gudunmawar da take bayarwa ga ƙasar mu a shekaru 25 masu zuwa da ma bayan haka. Waɗannan nasarori sun cancanci caffa da yawan yabo.”

Yayin da yake warware wani kuskuren fahimta game da Nijeriya a ƙasashen waje, Idris ya jaddada cewa ƙasar nan ba mai tauye ‘yancin addini ba ce, kuma ya tabbatar da cewa irin wannan ‘yanci ya samu cikakken tanadi a kundin tsarin mulki.

Ya jaddada cewa akwai ƙalubalen tsaro, amma ya ce ƙoƙarin gwamnati na kawo ɗa’a yana haifar da sakamako.

Ya gargaɗi masu yaɗa labarai marasa inganci da ke nuna Nijeriya ta wani mummunan salo, wanda hakan kan jawo matsala a hulɗar ta da abokan ta, musamman Amurka.

Ya roƙi ƙungiyoyi masu zaman kan su da su taimaka wajen gyara irin wannan mummunar fassarar ta hanyar amfani da hujjoji na gaskiya waɗanda za su ba su damar taka muhimmiyar rawa ta gini da jagoranci wajen sake fasalin labaran bogi da ake yaɗawa.

Minista da Uban Taron suna gaisawa

Yayin da ya tabbatar da nauyin da gwamnati take da shi na kare ‘yan ƙasa, musamman yara, ya jaddada cewa “ya kamata a kiyaye yaran mu a makarantun su, a cikin al’ummomin su, da kuma a gidajen su,” tare da jaddada sanarwar da Shugaba Tinubu ya yi kwanan nan kan dokar ta-ɓaci a fannin tsaro.

Ministan ya bayyana cewa matakan dokar ta-ɓaci sun haɗa da ɗaukar sababbin jami’ai a hukumomin tsaro, tallafa wa rundunonin tsaro na jihohi, da kuma tura ƙudirin doka domin kafa ‘yan sandan jihohi.

Ya bayyana wannan sanarwa a matsayin muhimmin mataki na juyin-juya-hali a yaƙi da ta’addanci da ‘yan bindiga.

Ya yi kira ga ƙungiyoyi masu zaman kan su (CSOs) da su zurfafa goyon bayan su ga shugabanci na fayyace komai, ‘yancin kafafen yaɗa labarai, ilimin zamani na dijital, da cigaban al’umma, tare da tabbatar da cewa gudunmawar ActionAid a waɗannan fannoni “na cike da muhimmanci kuma ba za a iya musanta ta ba” wajen cigaban ƙasa.

Tags: ActionAid Nigeriacika shekaruMohammed Idrisƙungiya
Previous Post

‘Yar aiki ta daɓa wa ’yar masu gida wuƙa ta kashe ta, sannan ta kashe kan ta

Next Post

CBN ya umurci bankuna su janye tallace-tallace masu ɗauke da ninanci da yaudarar kwastomomi

Related Posts

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Next Post
CBN ya tashi haiƙan: Malejin farashin kayayyaki ya ƙara yin ƙasa zuwa kashi 16.05, yayin da asusun kuɗaɗen waje ya kai dala biliyan 46.7

CBN ya umurci bankuna su janye tallace-tallace masu ɗauke da ninanci da yaudarar kwastomomi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!