• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Kotu ta ɗaure tsohon muƙaddashin Akanta-Janar Nwabuoku shekaru 72 a gidan yari

ALI KANO by ALI KANO
March 23, 2026
in Labarai
A A
0
Kotu ta ɗaure tsohon muƙaddashin Akanta-Janar Nwabuoku shekaru 72 a gidan yari
Mista Chukwunyere Anamekwe Nwabuoku

Mista Chukwunyere Anamekwe Nwabuoku

Wata Babbar Kotun Tarayya da ke zama a Abuja ta yanke wa tsohon muƙaddashin Akanta-Janar na Tarayya, Mista Chukwunyere Anamekwe Nwabuoku, hukuncin ɗaurin shekaru 72 a gidan yari kan badaƙalar Naira miliyan 868.46.

A wata sanarwa da ta fitar a ranar Litinin ta shafin ta na X (wanda a da ake kira Twitter), Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziki Ta’annati (EFCC) ta tabbatar da hukuncin da aka yanke wa Mista Nwabuoku bisa laifin wanke kuɗaɗe, bayan kotu ta same shi da laifi a duk tuhume-tuhumen da ake masa.

“Hukumar EFCC ta gurfanar da tsohon muƙaddashin Akanta-Janar na Tarayya, Chukwunyere Anamekwe Nwabuoku, a gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja kan laifin wanke kuɗaɗe da ya kai Naira miliyan 868.46, inda aka same shi da laifi tare da yanke masa hukuncin ɗaurin shekaru 72 a gidan yari,” inji hukumar.

A cewar EFCC, laifin ya saɓa wa sashe na 18 na Dokar Hana Wanke Kuɗaɗe ta shekarar 2011 (wadda aka gyara da Dokar lamba ta 1 ta 2012), kuma ana hukunta shi a ƙarƙashin sashe na 15(3) na dokar.

Hukumar ta ce Mista Nwabuoku ya aikata laifukan ne yayin da yake aiki a matsayin Daraktan Kuɗi da Asusun Ma’aikatar Tsaro tsakanin shekarar 2019 zuwa 2021.

Tsohon Akanta-Janar ɗin ya gabatar da buƙatar cewa babu hujjar tuhuma a kan sa, amma kotu ta yi watsi da ita a watan Nuwamba 2025.

An naɗa Mista Nwabuoku a matsayin muƙaddashin Akanta-Janar na Tarayya ne a ranar 20 ga Mayu, 2022, ta hannun marigayi Shugaba Muhammadu Buhari, bayan dakatar da Mista Ahmed Idris bisa zargin badaƙalar Naira biliyan 80.

Sai dai an tsige shi daga muƙamin a watan Yuli 2022, bayan makonni kaɗan da karɓar aiki, sakamakon rahotannin cewa EFCC tana binciken sa.

Shi ne sabon fitaccen mutum a cikin manyan mutane da aka yanke wa hukunci, bayan da a makon da ya gabata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta yanke wa tsohon Manajan Darakta na Bankin Fitar da Kayayyaki na Nijeriya (NEXIM), Mista Robert Orya, hukuncin ɗaurin shekaru 490 a gidan yari bayan samun sa da laifi a badaƙalar Naira biliyan 2.4.

A wata sanarwa da ta wallafa a shafin ta na X a ranar Alhamis, hukumar yaƙi da cin hanci ta tabbatar da cewa Mai Shari’a F.E. Messiri na Kotun Abuja ya yanke wa tsohon shugaban NEXIM ɗin, wanda ya yi aiki daga 2011 zuwa 2016, hukuncin ɗaurin shekaru 10 kan kowanne daga cikin tuhume-tuhume 49 da ake masa a shari’ar badaƙalar Naira biliyan 2.4.

Tags: Chukwunyere Anamekwe Nwabuokuhukuncikotuɗauri
Previous Post

Mutum 10 sun mutu a haɗarin tirela a hanyar Tafa, Jihar Neja

Next Post

Nijeriya ta ƙara ƙarfafa hulɗa da Tarayyar Turai kan tsaro

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Nijeriya ta ƙara ƙarfafa hulɗa da Tarayyar Turai kan tsaro

Nijeriya ta ƙara ƙarfafa hulɗa da Tarayyar Turai kan tsaro

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!