Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gana da babbar jami’ar Tarayyar Turai (EU) mai kula da harkokin waje da tsaro, Kaja Kallas, a wani muhimmin taro da aka gudanar a gidan sa da ke Legas.
A yayin ganawar, Shugaban Ƙasa tare da mai ba shi shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, sun tattauna kan hanyoyin ƙarfafa dangantaka tsakanin Nijeriya da Tarayyar Turai, musamman a fannonin tsaro, musayar bayanan sirri, da tabbatar da zaman lafiya a yankin.
Ziyarar ta Kaja Kallas tana nuni da yadda hulɗar Niieriya da Tarayyar Turai take ƙara ƙarfi, musamman wajen haɗa kai don yaƙi da ta’addanci, inganta tsaron yanar gizo, da kuma daƙile laifuffukan ƙetare iyakoki.
Haka zalika, an jaddada muhimmiyar rawar da Ribadu yake takawa wajen tsara manufofin tsaro na ƙasa da kuma jagorantar haɗin gwiwa da ƙasashen waje domin tunkarar barazanar tsaro.
Gwamnatin Nijeriya tana ci gaba da ƙoƙarin haɗa kai da ƙasashen duniya domin magance matsalolin tsaro da ke ƙara tasowa, tare da ƙarfafa alaƙa da Tarayyar Turai







