• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Ƙasashen Duniya

Ayatollah Ali Khamenei: Jagoran jajircewar Iran

New Citizen Hausa by New Citizen Hausa
March 1, 2026
in Ƙasashen Duniya
A A
0
Ayatollah Ali Khamenei: Jagoran jajircewar Iran
Ayatollah Ali Khamenei, jagoran Iran

Ayatollah Ali Khamenei, jagoran Iran

An kashe jagoran koli na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, a wani hari da Isra’ila da Amurka suka kai. Ya rasu yana da shekaru 86.

Kafofin watsa labaran gwamnatin Iran sun tabbatar da mutuwar sa da sanyin safiyar yau Lahadi, bayan Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa an kashe Khamenei ne a wani harin sama na haɗin gwiwa tsakanin Amurka da Isra’ila da ya auka gidan sa a jiya Asabar.

“An sanar da al’ummar Iran cewa Mai Girma Babban Ayatollah Imam Sayyid Ali Khamenei, Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci, ya yi shahada a harin haɗin gwiwa da Amurka da gwamnatin Sahyoniyawa suka kai da safiyar Asabar, 28 ga Fabrairu,” inji kamfanin dillancin labarai na Tasnim mai alaƙa da gwamnati.

Kafofin gwamnati sun kuma ce an kashe ɗiyar sa, surukin sa da jikan sa a harin.

Tun da fari, Trump ya ce Khamenei da wasu jami’an Iran “ba su iya tserewa daga bayanan sirrin Amurka da ingantattun na’urorin bibiyar diddigi ba.”

Shi dai Khamenei, ya karɓi ragamar mulki a Iran ne a 1989 bayan rasuwar Ayatollah Ruhollah Khomeini, jagoran da ya jagoranci juyin juya halin Musulunci shekaru goma kafin haka.

Duk da cewa Khomeini shi ne ginshiƙin aƙidar juyin juya halin da ya kawo ƙarshen mulkin sarautar Pahlavi, Khamenei ne ya gina ƙarfin soja da na rundunonin sa-kai da suka zama ginshiƙin tsaron Iran da kuma tasirin ta a waje.

Kafin ya zama jagoran ƙoli, sai da ya shugabanci Iran a matsayin shugaban ƙasa a lokacin yaƙin zubar da jini da Iraƙi a shekarun 1980. Wannan yaƙi mai tsawo, tare da jin kaɗaici da dama daga cikin ‘yan Iran suka ji yayin da ƙasashen Yamma ke goyon bayan Saddam Hussein, ya ƙara zurfafa rashin yarda da ƙasashen Yamma da Amurka a zuciyar sa, inji masana.

Wannan ra’ayi ne ya zama ginshiƙin mulkin sa na tsawon shekaru da ya tabbatar da cewa Iran dole ta kasance cikin shiri na kare kan ta daga barazanar waje da cikin gida.

Wasu na kallon Iran a matsayin mai mulkin addini kawai, amma a zahiri Khamenei shugaba ne da ya fito daga yanayin yaƙi, wanda ya ɗauki cewa Iran na cikin haɗari kuma tana buƙatar tsaro mai ƙarfi.

A ƙarƙashin wannan hangen nesa, Rundunar Kare Juyin Juya Hali ta Musulunci (IRGC) ta zama babbar cibiyar tsaro, siyasa da tattalin arziki, tare da faɗaɗa tasirin Iran a yankin.

Mulkin sa ya fuskanci manyan ƙalubale, ciki har da zanga-zangar 2009 bayan zaɓen da aka ce an tafka maguɗi, da kuma zanga-zangar 2022 kan haƙƙoƙin mata. A lokuta da dama, hukumomi sun murƙushe masu zanga-zanga da ƙarfi.

An haifi Khamenei a 1939 a birnin Mashhad mai tsarki a arewa maso gabashin Iran. Ya yi karatun addini tun yana ƙarami, kuma daga bisani ya shiga gwagwarmayar adawa da sarautar Pahlavi. An kama shi sau da dama tare da tura shi gudun hijira kafin juyin juya halin 1979.

Bayan kifar da mulkin sarauta, ya taka muhimmiyar rawa wajen kafa sabuwar Iran, inda ya riƙe muƙaman ministan tsaro da kuma jagoran sallar Juma’a a Tehran. A 1981, ya tsira daga yunƙurin kashe shi, amma ya rasa yin amfani da hannun sa na dama. A wannan shekarar ne kuma ya zama shugaban ƙasa.

Ayatollah Ali Khamenei ya rasu yana da shekaru 86

Bayan rasuwar Khomeini a 1989, majalisa ta naɗa shi jagoran ƙoli, duk da cewa bai cika sharuɗɗan addini mafi girma ba a lokacin. Duk da haka, jagorancin sa bai kasance na alama kawai ba.

Ya mayar da hankali wajen gina ƙarfin soja da tsarin “tsayin daka” ga Yamma, tare da haɗa kai da ƙungiyoyin ƙawance a yankin wanda ake kira “axis of resistance”. Wannan ya hada da ƙungiyoyi a Lebanon, Syria, Falasdinu da Yemen.

A 2015, ya amince da yarjejeniyar nukiliya da ƙasashen duniya (JCPOA) domin rage takunkumi, amma Amurka ta fice daga yarjejeniyar a 2018 a ƙarƙashin Trump, lamarin da ya sake tsananta rikici.

A cikin shekarun baya-bayan nan, takunkumi mai tsanani da hauhawar farashi sun haddasa zanga-zanga a faɗin ƙasar, wacce aka murƙushe da ƙarfi.

Mata suna nuna alhini a Iran (Hoto: Majid Asgaripour/WANA via REUTERS)

A ranar 28 ga Fabrairu, Trump ya ba da sanarwar fara “babban aikin soji” a Iran, yana mai kira ga canjin gwamnati.

“Lokacin ‘yancin ku ya zo,” inji Trump lokacin da yake jawabi ga al’ummar Iran. “Idan muka gama, ku karɓi mulkin ku — naku ne.”

Mun fassaro daga rahoton Al Jazeera

Tags: AliKhameneiAmurkaIranIsra'ilayaƙi
Previous Post

Ministan Yaɗa Labarai ya buƙaci matasa su riƙa tantance sahihancin labari kafin su yaɗa shi

Next Post

Bayan shekaru 10, Nijeriya ta sake ƙetare kashi 4% na haɓakar tattalin arziki a ƙarshen 2025

Related Posts

Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce
Ƙasashen Duniya

Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce

April 24, 2026
Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma
Ƙasashen Duniya

Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma

April 20, 2026
Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa
Ƙasashen Duniya

Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa

April 20, 2026
Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran
Ƙasashen Duniya

Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran

April 18, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Ƙasashen Duniya

CBN na shirin kafa kwamitin sulhu don warware rikice-rikicen masu taurin bashi

April 17, 2026
Iran ta kakkaɓo jirgin yaƙin Amurka a sararin samaniyar ta
Ƙasashen Duniya

Iran ta kakkaɓo jirgin yaƙin Amurka a sararin samaniyar ta

April 3, 2026
Next Post
Nijeriya ta rattaba hannu kan babbar yarjejeniyar zuba jari a fannin kiwon lafiya

Bayan shekaru 10, Nijeriya ta sake ƙetare kashi 4% na haɓakar tattalin arziki a ƙarshen 2025

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!