Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki, Mista Wale Edun, ya yi maraba da sababbin bayanai daga Hukumar Ƙididdigar ta Kasa (NBS) da ke nuna cewa tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka da kashi 4.07 cikin ɗari a ƙarshen 2025.
Wannan shi ne karo na biyu a cikin shekaru goma, idan ban da haɓakar da aka samu bayan cutar COVID-19, da aka samu haɓakar tattalin arziki fiye da kashi 4 cikin ɗari.
Wannan cigaban ya biyo bayan ƙaruwar kashi 4.23% da aka samu a zango na biyu na 2025, wanda ya nuna cigaba daga kashi 3.76% da aka samu a zango na uku na 2024.
Haka kuma cigaban ya nuna ƙaruwar kwanciyar hankali a tsarin tattalin arziki da kuma tasirin sauye-sauyen da ake yi ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
An samu haɓaka a manyan ɓangarorin tattalin arziki guda uku a ƙarshen shekarar waɗanda suka haɗa da:
- Aikin Gona: Ya haɓaka da 4.0%, idan aka kwatanta da 2.54% a ƙarshen 2024. An samu wannan haɓakar ne saboda ingantuwar tsaro a yankunan da ake samar da abinci da kuma samun sauƙin samun kayayyakin noma.
- Masana’antu: Sun haɓaka da 3.88%, idan aka kwatanta da 2.49% a daidai irin wannan lokacin a 2024. An samu wannan haɓakar ne saboda ingantuwar hadahadar kuɗaɗen ƙasashen waje, sauye-sauye a fannin makamashi, da kuma ƙaruwar ƙwarin gwiwar masu zuba jari.
- Ayyukan ‘Yan Kasuwa: Sun haɓaka da 4.15%, wanda ya nuna cigaban haɓaka a fannin kuɗi, sadarwa, ciniki, da kuma fasahar zamani.
Kimanin ɓangarori 30 ne suka samu haɓaka fiye da kashi 3%, wanda ya nuna fadin haɓakar tattalin arzikin ƙasa da kuma ƙaruwar rarrabuwar sa.
A dukkan tsawon 2025, tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka da kashi 3.87%, idan aka kwatanta da 3.38% a 2024.
Girman tattalin arzikin ƙasar nan ya ƙaru zuwa naira tiriliyan 441.5, idan aka kwatanta da naira tiriliyan 372.8 a 2024.
Wannan haɓakar ta nuna ingantuwar haɗin kai a ɓangaren kasafin kuɗi, kiyaye kuɗaɗen kashewa, ƙarfafa hanyoyin samun kuɗaɗen shiga, da kuma cigaba da sauye-sauyen tsarin tattalin arziki don maido da sahihancin tattalin arziki.
Ministan ya ƙara da cewa waɗannan bayanan suna ƙarfafa ƙwarin gwiwar masu zuba jari na gida da na waje, kuma suna nuna cewa shirin sauye-sauyen Nijeriya yana samun nasara.
Wata sanarwar gwamnati ga manema labarai ta ce, “Ma’aikatar Kuɗi tana ci gaba da jajircewa wajen aiwatar da sauye-sauye, daidaiton hukumomi, da kuma tattaunawa ta gaskiya tare da masu ruwa da tsaki.”







