• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Ƙasashen Duniya

Gwamnati ta ba ‘yan Nijeriya mazauna Iran da ƙasashen Larabawa shawarwari 5 kan rikicin Gabas Ta Tsakiya

Wakilin Mu by Wakilin Mu
February 28, 2026
in Ƙasashen Duniya
A A
0
Gwamnati ta ba ‘yan Nijeriya mazauna Iran da ƙasashen Larabawa shawarwari 5 kan rikicin Gabas Ta Tsakiya
Mutane na gudu don neman mafaka sakamakon fashewar bamabamai a Tehran a safiyar yau (Hoto: Majid Asgaripour/WANA/Reuters)

Mutane na gudu don neman mafaka sakamakon fashewar bamabamai a Tehran a safiyar yau (Hoto: Majid Asgaripour/WANA/Reuters)

Mutane na gudu don neman mafaka sakamakon fashewar bamabamai a Tehran a safiyar yau (Hoto: Majid Asgaripour/WANA/Reuters)

Gwamnatin Tarayya ta buƙaci ɗaukacin ‘yan Nijeriya dake zaune a ƙasar Iran da sauran ƙasashen yankin Tekun Fasha da su kasance cikin tsananin sa ido da kiyaye kai, biyo bayan takun-saƙa da hare-haren soji da suka ɓarke a yankin.

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar a ranar Asabar, 28 ga Fabrairu, 2026, wadda kakakin ma’aikatar, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, ya sanya wa hannu, gwamnatin ta bayyana cewa tana sanya idanu sosai kan yadda al’amura ke sauyawa bayan hare-haren da Isra’ila da Amurka suka kai kan wasu wurare a Iran, da kuma martanin da ita ma Iran ɗin ta mayar.

Don tabbatar da tsira da lafiyar ‘yan ƙasar nan, ma’aikatar ta fitar da wasu shawarwari guda biyar kamar haka:

* Gwamnati ta shawarci ‘yan Nijeriya da su guji zirga-zirga a kusa da sansanonin soji, gine-ginen gwamnati, ko wuraren da ake ganin za su iya zama matattarar rikici.

* An buƙaci mutane da su zauna a gida muddin ba wata muhimmiyar buƙata ce ta fitar da su ba, sannan su guji shiga taron jama’a ko zanga-zanga.

* An buƙaci ‘yan kasa da su kiyaye dukkan dokoki da matakan tsaro da hukumomin ƙasashen da suke ciki suka gindaya.

* Ma’aikatar ta buƙaci mutane da su riƙa sauraron kafafen yaɗa labarai na ƙasa da ƙasa masu gaskiya, sannan su kiyayi yaɗa labaran bogi.

* Sanarwar ta tabbatar da cewa ofisoshin jakadancin Nijeriya da ke Tehran (Iran), Ƙatar, Bahrain, Kuwait, Haɗɗaɗiyar Daular Larabawa (UAE), da Saudi Arabiya suna cikin shirin ko-ta-kwana don tallafa wa duk wani ɗan Nijeriya da ya shiga cikin matsala.

A ƙarshe, gwamnatin ta yi kira ga ɗaukacin ɓangarorin da rikicin ya shafa da su kwantar da hankalin su, su ajiye makamai su koma kan teburin tattaunawa domin samar da zaman lafiya a duniya.

Ta kuma sake jaddada cewa kare rayukan ‘yan Nijeriya a duk inda suke a faɗin duniya shi ne babban burin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Tags: AmurkaGulfIranshawarwariyaƙi
Previous Post

Ɗan Majalisar Amurka Riley Moore ya zargi ‘yan Chana da tallafa wa ta’addanci kan Kiristocin Nijeriya

Next Post

Ministan Yaɗa Labarai ya buƙaci matasa su riƙa tantance sahihancin labari kafin su yaɗa shi

Related Posts

Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce
Ƙasashen Duniya

Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce

April 24, 2026
Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma
Ƙasashen Duniya

Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma

April 20, 2026
Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa
Ƙasashen Duniya

Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa

April 20, 2026
Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran
Ƙasashen Duniya

Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran

April 18, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Ƙasashen Duniya

CBN na shirin kafa kwamitin sulhu don warware rikice-rikicen masu taurin bashi

April 17, 2026
Iran ta kakkaɓo jirgin yaƙin Amurka a sararin samaniyar ta
Ƙasashen Duniya

Iran ta kakkaɓo jirgin yaƙin Amurka a sararin samaniyar ta

April 3, 2026
Next Post
Ministan Yaɗa Labarai ya buƙaci matasa su riƙa tantance sahihancin labari kafin su yaɗa shi

Ministan Yaɗa Labarai ya buƙaci matasa su riƙa tantance sahihancin labari kafin su yaɗa shi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!