Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya taya waɗanda suka yi nasara a zaɓuɓɓukan da aka gudanar jiya Asabar a Babban Birnin Tarayya (FCT) da jihohin Kano da Ribas murna.
Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta gudanar da zaɓe a ƙananan hukumomi shida na FCT, tare da zaɓen cike gurbi a mazaɓun Ahoada East II da Khana II na Jihar Ribas, da kuma mazaɓun Kano Municipal da Ungogo a Jihar Kano.
Shugaba Tinubu ya buƙaci waɗanda suka lashe zaɓen da su yi aiki da kyautatawa, kishin ƙasa da kuma sadaukar da kai, yana mai jaddada cewa amanar da al’umma suka ba su wata amana ce mai tsarki da ya wajaba su kiyaye.
Haka kuma, ya yaba wa Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, bisa irin nasarorin da ya samu a yankin, wanda ya ce sun taimaka wajen samar wa jam’iyyar APC gagarumar nasara a zaɓen.
Shugaban ya kuma taya shugabannin APC na ƙasa da na jihohin Kano da Ribas, tare da dukkan membobin jam’iyyar, murnar nasarorin da aka samu a zaɓen.
Ya yaba wa INEC, jami’an tsaro da masu kaɗa ƙuri’a bisa gudanar da zaɓen cikin lumana da nasara, tare da yaba wa dukkan ‘yan takarar da suka nuna jajircewa da bin doka yayin fafatawar zaɓen.
A cewar sa, nasarar gudanar da zaɓuɓɓukan cikin nasara na ƙara ƙarfafa dimokiraɗiyya a ƙasar nan, yana mai kira ga INEC da ta ci gaba da inganta ayyukan ta domin samar da sahihin tsarin zaɓe a nan gaba.






