• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Mahanga

Musulunci Da Masu Yi Masa Zagon Ƙasa A Nijeriya

Aliyu Haidar by Aliyu Haidar
February 15, 2026
in Mahanga
A A
0
Musulunci Da Masu Yi Masa Zagon Ƙasa A Nijeriya
Musulmi yana addu'a

Musulmi yana addu'a

Alhamdu lillah, dukkan yabo da godiya sun tabbata ga Allah, Ubangijin talikai.

Ya ku ’yan uwa, muna rayuwa ne a wani zamani da wasu suka mayar da sukar Musulunci a matsayin hanyar neman suna da matsayi a idon duniya. Waɗannan masu adawa suna tsammanin cewa ta hanyar faɗin maganganu masu ɗaci da yaɗa ƙarairayi za su iya raunana gwiwar al’umma ko kuma su dusashe hasken addinin mu. Suna ƙoƙarin nuna addinin mu a matsayin wanda yake raguwa ko kuma wanda ke cike da tashin hankali, amma ƙoƙarin su tamkar busa ne ga rana da nufin kashe hasken ta—abu ne wanda ba zai taɓa yiwuwa ba.

Muna ganin hakan a sarari cikin ƙirƙirarren labarin nan na “kisan ƙare-dangi ga Kiristoci” (Christian genocide) a Nijeriya—wani labari da aka ƙirƙira don sauya rikice-rikicen karkara zuwa rikicin addini don cimma wata manufa. Ana tallata wannan labari zuwa ƙasashen waje, inda yake samun karɓuwa a wasu da’irori a Amurka, waɗanda ke amfani da hakan don neman tsoma bakin ƙasashen duniya a cikin al’amurran mu. Suna kau da kai ga gaskiyar cewa mu ma Musulmi muna fuskantar irin waɗannan matsalolin tsaro. Ba sa amfani da waɗannan kalaman don neman zaman lafiya, face dai don killace Musulmi da kuma haifar da ƙiyayya gare mu a idon duniya.

Duk da wannan ƙiyayya da aka tsara, gaskiya ba ta taɓa ja da baya. Ku duba yankunan kudancin ƙasar mu—wurare da wasu suka yi zargin cewa saƙon Musulunci ba zai taɓa kafuwa ba. Maimakon haka, yau muna ganin gagarumin canji mai ban-sha’awa. Musulunci yana yaɗuwa tamkar wutar daji.

Wannan haɓaka ba ta hanyar ƙarfi take ko yaudarar siyasa ba, a’a, sai dai ta hanyar ƙarfin kyawawan ɗabi’u, da kyakkyawar mu’amalar Musulmi, da kuma natsuwar da Alƙur’ani yake sanyawa a cikin zukata.

Munafiki zai iya ci gaba da yaƙin neman ƙeta, masu son zuciya kuma su ci gaba da sayar da gurtaɓatattun labaran su a ƙasashen waje, amma sun mance da wata gaskiya ɗaya tabbatacciya: Allah ne mai kare hasken Sa. Yayin da suke shagaltuwa da ƙirƙirar matsaloli don neman matsayi, zukatan masu gaskiya kuma buɗewa suke yi. Duk wani yunƙuri na daƙile wannan addini, ƙara masa ƙarfi da juriya yake yi.

Yayin da suke shagaltuwa da ƙirƙirar matsaloli don neman matsayi, zukatan masu gaskiya kuma buɗewa suke yi. Duk wani yunƙuri na daƙile wannan addini, ƙara masa ƙarfi da juriya yake yi.

Saboda haka, bari mu kasance masu jajircewa. Bari martanin mu ga ɗacin maganganun su ya kasance ta hanyar kyautatawa; martanin mu ga ƙarairayin su kuma ya kasance ta hanyar riƙo da gaskiya.

Dole ne mu zama shaida mai rai da ke nuna cewa ƙarairayin su ba gaskiya ba ne. Domin lallai alƙawarin Allah gaskiya ne: “Suna nufin su kashe hasken Allah da bakunan su, amma Allah zai cika hasken Sa, ko da kuwa kafirai sun ƙi.”

Muna roƙon Allah Ya tabbatar da mu a kan hanya madaidaiciya, Ya kare mu daga makircin maƙaryata, kuma Ya ci gaba da albarkaci yaɗuwar wannan addini a kowane sako na wannan ƙasa.

* Aliyu Haidar, yana zaune a Badikko, Kaduna

Tags: IslammaƙarƙashiyaMusulunci
Previous Post

Cewar Shugaba Tinubu: Bikin Argungu shaida ce ta dawowar zaman lafiya, na yi alƙawarin goyon baya ga noma da yawon buɗe ido

Next Post

Tinubu ya yi wa ‘yan kasuwar Kano jaje kan gobarar Singa, ya ba da umurnin bincike

Related Posts

Hausa Zalla Ko Zallar Jahilci?
Mahanga

Hausa Zalla Ko Zallar Jahilci?

March 29, 2026
Mahanga

Yadda Aka Raba Musulmi Da Ƙur’ani

February 22, 2026
Taƙaddamar Imam Ghazali Da Ibn Rushud A Kan Ruhi (Rai)
Mahanga

Taƙaddamar Imam Ghazali Da Ibn Rushud A Kan Ruhi (Rai)

February 18, 2026
Sarkin Adabi: Mafi Girman Sarautar Fasaha
Mahanga

Sarkin Adabi: Mafi Girman Sarautar Fasaha

February 13, 2026
Muhimman Shawarwarin Tsaro Ga Magidanta Da Iyalai
Mahanga

Muhimman Shawarwarin Tsaro Ga Magidanta Da Iyalai

January 20, 2026
Tinubu ya sha alwashin ganin bayan maƙiyan Nijeriya, ya girmama marigayi Abubakar Audu
Mahanga

Muhimmin lokaci a Nijeriya: Hujjar da ta sa hanyar da aka ɗauka ita ce mai ɓullewa

January 4, 2026
Next Post
Tinubu ya yi wa ‘yan kasuwar Kano jaje kan gobarar Singa, ya ba da umurnin bincike

Tinubu ya yi wa ‘yan kasuwar Kano jaje kan gobarar Singa, ya ba da umurnin bincike

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!