• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Tsaro

Tsaro: Nijeriya da Amurka sun ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa don kare ’yancin addini da rayukan jama’a

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
January 22, 2026
in Tsaro
A A
0
Tsaro: Nijeriya da Amurka sun ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa don kare ’yancin addini da rayukan jama’a
Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Shugaba Donald Trump

Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Shugaba Donald Trump

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta sake jaddada ƙudirin ta na kare rayuka da dawo da tsaro a faɗin ƙasar nan, yayin da Nijeriya da Amurka suka ƙarfafa haɗin gwiwa kan tsaro, ’yancin addini da kare fararen hula.

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Abuja, yayin da yake yi wa manema labarai bayani bayan taron haɗin gwiwa tsakanin Nijeriya da Amurka, wanda aka gudanar a Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro (ONSA), Malam Nuhu Ribaɗu.

Taron ya mayar da hankali ne kan batun sanya Nijeriya a matsayin “Ƙasar da ke da Damuwa ta Musamman”.

A cewar Ministan, wannan zama shi ne karo na uku da aka yi irin wannan ganawa tsakanin Nijeriya da manyan jami’an Amurka tun daga watan Nuwamba 2025, lamarin da ke nuna ƙarfi da ɗorewar dangantakar ƙasashen biyu.

Ya ce wannan haɗin gwiwar yana nuna matsaya ɗaya kan kare ’yancin addini, kare farar hula, da kuma dangantaka mai ma’ana wadda aka gina kan gaskiya da amana.

Malam Nuhu Ribadu da Mataimakiyar Sakataren Harkokin Wajen Amurka kan Harkokin Siyasa, Allison Hooker, su ne suka jagoranci zaman taron.

Idris ya bayyana cewa haɗin gwiwar tsaro da Amurka ya haifar da nasarori na gaske ga tsarin tsaron Nijeriya.

Ya ce sojojin Nijeriya da sauran hukumomin tsaro suna aiki kafaɗa da kafaɗa da takwarorin su na Amurka ta hanyar musayar bayanan sirri da haɗin kai a ayyukan tsaro, wanda ya ƙarfafa manyan ayyuka kamar Operation Haɗin Kai a Arewa-maso-gabas da Operation Fasan Yamma.

Ministan ya ƙara da cewa Amurka ta yi alƙawarin gaggauta isar da sauran kayan aikin soja da Nijeriya ta saya cikin shekaru biyar da suka gabata, ciki har da jiragen leƙen asiri marasa matuƙa (drones), helkwaftoci, kayayyakin aiki, sassan gyaran makamai da na’urorin tallafi.

Dangane da matakan tsaro a cikin gida, Idris ya tunatar da cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci ta tsaro a wasu yankuna masu haɗari, inda ya ba da izinin ƙara haɗin gwiwar jami’an tsaro, tare da umurtar a ci gaba da tura dakarun tsaro zuwa wuraren da suka fi buƙatar kariya.

Ya ce an bai wa hukumomin tsaro umurni bayyananne na kare al’umma da kuma gaggauta ɗaukar mataki kan kowace barazana.

Ministan ya kuma bayyana cewa Gwamnatin Tarayya tana ƙarfafa tsarin gargaɗin wuri-wuri tare da samar da kundin bayanai na ƙasa guda ɗaya da zai tattara sahihan alƙaluma kan mutuwar mutane da asarar rayuka sakamakon tashin hankali.

A cewar sa, hakan zai taimaka wajen yanke shawara mai inganci, tabbatar da bin ƙa’ida, da kuma inganta martanin tsaro.

Ya jaddada cewa tabbatar da adalci muhimmin ginshiƙi ne a dabarun tsaron gwamnati, yana mai cewa Ma’aikatar Shari’a, Hukumar DSS da Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya suna ci gaba da bincike da gurfanar da masu laifin ta’addanci domin tabbatar da adalci da hukunci.

Idris ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su ci gaba da haƙuri tare da ba gwamnati goyon baya yayin da ake aiwatar da gyare-gyaren tsaro, yana mai tabbatar da cewa dukkan matakan da ake ɗauka a yau suna da nufin tabbatar da ingantaccen tsaro ne a ƙasar nan.

Manyan jami’an gwamnati da suka halarci taron sun haɗa da Ministan Tsaro, Janar Christopher Gwabin Musa (mai ritaya); Babban Hafsan Tsaro, Janar Olufemi Oluyede; Ministan Kasafi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Abubakar Atiku Bagudu; Ƙaramar Ministar Harkokin Kuɗi, Dakta Doris Uzoka-Anite; Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo; Sufeto-Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun; da Kwanturola-Janar na Hukumar Kwastam ta Nijeriya, Bashir Adewale Adeniyi.

Tawagar Amurka kuma ta haɗa da Mataimakiyar Sakatariyar Harkokin Wajen Amurka mai Kula da Harkokin Siyasa, Allison Hooker; Babban Jami’in Gudanarwa na Ofishin Jakadancin Amurka a Nijeriya, Keith Heffern; Mataimakin Sakataren Harkokin Waje mai Kula da Dimokiraɗiyya, ’Yancin Ɗan’adam da Ƙwadago, Riley Barnes; Mataimakin Kwamandan AFRICOM, Laftanar-Janar John Brennan, tare da sauran manyan jami’ai daga Ma’aikatun Harkokin Waje da Tsaro na Amurka.

Tags: haɗingwiwaMohammedIdrisShugaba BolaAhmedTinubuShugabaDonaldTrumptarotsaro
Previous Post

Bikin Argungu alama ce ta haɗin kan ƙasa da samun karɓuwa a idon duniya – Gwamnatin Tarayya

Next Post

Tinubu ya ba da umurnin a fara aikin haƙo man fetur a Ogun

Related Posts

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma
Tsaro

Zargin juyin mulki: Sojoji sun ƙaddamar da Babbar Kotun Soja, sun fara shari’ar jami’an da ake tuhuma

April 25, 2026
Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos
Tsaro

Sojoji sun kama ɗan tasi da ɗimbin alburusai da kayayyakin haɗa bamabamai a hanyar Kaduna zuwa Jos

April 17, 2026
‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya
Tsaro

‘Yan sanda sun miƙa wani da ake zargi da kisan kai ga hukumomin Birtaniya

April 16, 2026
Sojoji sun ragargaji maɓoyar ‘yan ta’adda a dajin Bauchi, sun kamo iyalan su
Tsaro

Sojoji sun ragargaji maɓoyar ‘yan ta’adda a dajin Bauchi, sun kamo iyalan su

April 15, 2026
Nijeriya ba za ta miƙa wuya ga ’yan ta’adda ba – Gwamnatin Tarayya
Tsaro

Gwamnatin Tarayya ta kare harin jirgin sama a Jilli, ta ba da umurnin bincike

April 14, 2026
An kashe kwamanda da sojoji shida ta hanyar bam a Borno
Tsaro

An kashe kwamanda da sojoji shida ta hanyar bam a Borno

April 13, 2026
Next Post
Tinubu ya ba da umurnin a fara aikin haƙo man fetur a Ogun

Tinubu ya ba da umurnin a fara aikin haƙo man fetur a Ogun

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!