UWARGIDAN Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta bayyana aniyar ta na ganin an kawar da cutar tarin fuka (TB) a Najeriya kafin shekarar 2030. Ta bayyana haka ne a wurin kaddamar da sabbin na’urorin gano cutar TB da aka samar domin inganta ganowa da magance cutar a faɗin ƙasar nan.
An gudanar da bikin ƙaddamarwar ne a Bwari, Abuja, inda aka bayyana cewa na’urorin an samar da su ne ta karkashin shirin Renewed Hope Initiative (RHI) da Sanata Oluremi Tinubu ke jagoranta, wanda ya cika alkawarin naira biliyan daya da aka yi a lokacin bikin ranar ciwon Tarin Fuka ta duniya a Sauka dake birnin tarayya.
A jawabin da ta gabatar ta bakin matar Gwamnan Jihar Kwara, Ambasada Olufolake Abdulrazaq, Sanata Tinubu ta ce da wannan cigaba, za a iya gane cutar cikin gaggawa a sassa da dama na ƙasar nan, musamman inda mutane ba su da isassun kayan gwaji.
Ta ce cutar TB na da magani, amma mutane da dama a Najeriya na mutuwa sanadiyyar rashin na’urorin tantance cutar da wuri.
Ta kuma jaddada buƙatar ƙara saka hannun jari daga cikin gida, samar da kuɗi, da ƙwarewa.
Ministan Lafiya da Jin Daɗin Al’umma, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya yaba wa Sanata Tinubu bisa jagoranci da jajircewar da ta nuna wajen yaƙi da cutar TB.
Ya ce Gwamnatin Tarayya na ci gaba da ɗaukar matakai don haɗa ayyukan yaki da TB cikin tsarin kula da lafiyar matakin farko da kuma ƙarfafa ɗaukar ma’aikatan lafiya.





