Tsohon Ministan Shari’a kuma Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, Alhaji Abubakar Malami, SAN, ya musanta zargin da ke yawo a kafafen yaɗa labarai cewa yana ɗaukar nauyin ta’addanci ko kuma an gano makamai a ofishin sa.
A cikin wata sanarwar manema labarai da hadimin sa na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Mohammed Bello Doka, ya fitar, tsohon ministan ya bayyana rahotannin a matsayin “zarge-zargen da ba a tantance ba da ake gabatarwa kamar gaskiya.”
Sanarwar ta ce: “Ba a taɓa samun hukunci a kan Abubakar Malami, SAN, kan kowane laifi ba. Duk da haka, wasu sassan kafafen yaɗa labarai na ci gaba da gabatar da zarge-zarge, bincike da hasashe a matsayin hujjar laifi, wanda hakan ya saɓa wa ƙa’idar ɗaukar mutum a matsayin marar laifi da kuma bin ƙa’ida kamar yadda Kundin Tsarin Mulki ya tanada.”
Doka ya rubuta cewa: “Muna ƙin yarda gaba ɗaya da iƙirarin cewa an gano wani tarin makamai ko harsasai a kowane gida da ke da alaƙa da Abubakar Malami, SAN.
“Wannan iƙirarin ƙarya ne, bai da tushe, kuma bai da goyon bayan kowace hukuma, takardar kotu ko sanarwar doka. Ba a taɓa sanar da iyalin sa ko lauyoyin sa a hukumance game da irin wannan bincike ba.
“Haka nan, mun ƙin yarda da duk wani zargi ko shaguɓe da ke danganta Abubakar Malami, SAN, da ta’addanci, ɗaukar nauyin ta’addanci ko wasu ayyuka masu alaƙa da hakan.
“An gabatar da irin waɗannan iƙirarin ba tare da ambaton ko mutum ɗaya ba, ko ƙungiya, ko mu’amala, ko kwanan wata, ko wata hujja mai tabbaci ba, lamarin da ya sa suke hasashe marasa ma’ana.”
A cewar sanarwar, “Tun bayan kama shi da DSS ta yi a ranar Litinin, an hana Abubakar Malami, SAN, samun damar ganawa da iyalin sa, tawagar lauyoyin sa da abokan hulɗar sa.
“Wannan tsawaita keɓancewa na tayar da sahihiyar damuwa game da lafiyar sa, walwalar sa da haƙƙoƙin sa da Kundin Tsarin Mulki ya tabbatar, ciki har da samun lauya da kuma hulɗa da iyali.
“Muna kuma nuna damuwa kan wahala da nauyin damuwa da aka jefa iyalin sa da ma’aikatan sa ciki sakamakon rahotannin da ke tayar da hankali da labaran da ba a tantance ba.
“Ya dace a lura cewa Abubakar Malami, SAN, babban jigo ne a jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), kuma ya bayyana a fili aniyar sa ta tsayawa takarar gwamnan Jihar Kebbi a zaɓen 2027.
“Bisa wannan tushe, ba za a iya yin watsi da alamar siyasa da ke kewaye da wannan batu ba. Dole ne hanyoyin shari’a su kasance masu zaman kan su daga tasirin siyasa.
“Abubakar Malami, SAN, na nan daram kan bin doka da oda da kuma ƙa’idojin shari’a. Muna kira ga kafafen yaɗa labarai da su dakatar da shari’ar kanun labarai, su bambanta zargi da gaskiya a sarari, kuma su bar hanyoyin shari’a su yi aikin su ba tare da son zuciya ba.”







