Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, haƙurin addini, da zaman lafiya, yana mai bayyana su a matsayin muhimman ginshiƙan tsaron ƙasa da ci gaba mai ɗorewa.
Shugaban Ƙasar ya yi kiran ne a ranar Litinin a yayin taron ƙasa da ƙasa karo na huɗu na Cibiyar Wayewar Musulunci da Tattaunawar Addinai da aka gudanar a Jami’ar Bayero da ke Kano.
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ne ya wakilci Shugaban Ƙasa a wurin taron.
Shugaban Ƙasa Tinubu ya jinjina wa Cibiyar Wayewar Musulunci da Tattaunawar Addinai, da kuma Masallacin Sultan Bello da ke Kaduna, bisa ci gaba da shirya tarukan tattaunawa tsakanin addinai, waɗanda ke bunƙasa zaman lafiya da ƙarfafa haɗin kan ƙasa.”
Ya ce, “Wannan taro na ci gaba da ɗaukaka manufofin zaman lafiya da haɗin kan ƙasar mu ta hanyar tattaunawa. Ina alfahari da wannan gayyata.”
Ya bayyana yadda taron ya mayar da hankali kan gadon marigayi Sheikh Mahmud Abubakar Gumi a matsayin abin da ya dace da lokaci kuma mai ilmantarwa, yana mai cewa fitaccen malamin addinin ya taka rawar gani sosai wajen ƙarfafa haɗin kan ƙasa a lokuta masu muhimmanci a tarihin Nijeriya.
“Sheikh Gummi ya fahimci inda addini da siyasa ke haɗuwa, kuma ya yi aiki kafaɗa da kafaɗa da mahukunta bayan samun ’yancin kai da kuma bayan yaƙin basasa domin inganta haɗin kai da zaman lafiya,” inji shi.
Tinubu ya bayyana Sheikh Gummi a matsayin fitaccen malami, mai kawo gyara, kuma jigo na ƙasa wanda tasirin sa ya wuce fagen addini kaɗai.
“Malami ne, mai gyara, mai ba da shawara, kuma marubuci ne mai hazaƙa. Ya koyar da tsararraki da dama su yi imani da rashin rarrabuwar Nijeriya, a fannin aiki da kuma a ibada,” inji Shugaban Ƙasar.
Dangane da ƙalubalen da ƙasar ke fuskanta a yanzu, Shugaba Tinubu ya buƙaci ’yan Nijeriya da su yi watsi da labaran da ke nuna ƙasar a matsayin wadda ba ta mutunta ’yancin addini.
“Dole ne mu ƙarfafa ƙudirin mu na gina ƙasa mai haɗin kai. Dole ne mu tunkari yunƙurin kwanan nan na ɓata sunan Nijeriya a matsayin ƙasar da ke tauye ’yancin addini,” inji shi.
Shugaban Ƙasar ya jaddada cewa tsaron ƙasa yana da alaƙa kai tsaye da haɗin kai da mutunta juna a tsakanin ’yan ƙasa.
“Tsaron ƙasar mu yana da alaƙa da haɗin kanmu, zaman tare, da mutunta bambancin addini. Dole ne mu haɗa kai mu fuskanci duk waɗanda ke neman raba kan mu,” inji shi.
Ya sake jaddada ƙudirin gwamnatin sa na kare rayuka da dukiyoyi tare da yaƙar laifuka a faɗin ƙasar.
“Gwamnati na na aiki tuƙuru wajen kare rayuka da dukiyoyi da kuma yaƙi da ta’addanci ta dukkan hanyoyin da muke da su,” inji Tinubu.
Ya bayyana cewa an tura sama da jami’an tsaron daji fiye da 7,000 waɗanda aka horar a faɗin ƙasar domin hana masu laifi amfani da hanyoyin dazuzzuka, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin kafa rundunar ’yan sandan jihohi domin tabbatar da tsaro a matakin al’umma, bisa tanadin kundin tsarin mulki.
Shugaban Ƙasar ya ƙara da cewa bayan ayyana dokar ta-ɓaci kan tsaro a watan Nuwamba 2025, an faɗaɗa kuma an ƙarfafa ayyukan tsaro a jihohin da ke fama da ’yan fashi da ta’addanci.
“Mun inganta ayyukan tsaro ta hanyar amfani da bayanan sirri domin tarwatsa cibiyoyin ’yan ta’adda da masu laifi,” inji shi.
Shugaban Ƙasa Tinubu ya kuma bayyana haɗin gwiwar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka, yana mai jaddada cewa haɗin gwiwar na mayar da hankali ne kan yaƙi da ta’addanci da kare fararen hula tare da mutunta ikon Nijeriya.
Ya kammala da kiran ’yan Nijeriya da su ɗaukaka kyawawan ɗabi’un su da zaman lafiya, yana mai bayyana haɗin kai a matsayin ginshiƙin dauwamammen zaman lafiya.
Manyan malamai da shugabannin addinin Musulunci da suka halarci taron sun haɗa da Shugaban Jama’atul Izalatul Bidi’a Wa’Ikamatul Sunnah (JIBWIS), Sheikh Abdullahi Bala Lau; Babban Limamin Jihar Kano, Farfesa Shehu Ahmad Galadanci; Mataimakin Shugaban Jami’ar Bayero, Kano, Farfesa Haruna Musa; Sheikh Ahmad Mahmud Gummi; da Janar Abdulkadir Mahmud Gummi (mai ritaya), da sauran su.







