• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda shirin CBN na ƙarfafa jarin bankuna zai fara samar da gagarumin tattalin arziki tun daga 2026

Nazari

ASHAFA MURNAI BARKIYA by ASHAFA MURNAI BARKIYA
January 26, 2026
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Kamfanonin ‘yan canji 82 kaɗai CBN ya ba lasin canjin kuɗin ƙasashen waje
Gwamnan CBN, Olayemi Cardoso, tare da bankin

Gwamnan CBN, Olayemi Cardoso, tare da bankin

Yanzu haka dai Babban Bankin Nijeriya (CBN) a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Olayemi Cardoso na ci gaba da ƙoƙarin tabbatar da kyakkyawan tsari da ƙa’idoji tare da ƙarfafa tsarin kuɗin Nijeriya, shirin sake ƙarfafa jarin bankuna da ake aiwatarwa na nuna aniyar CBN wajen kafa tsarin kuɗi mai ƙarfi da juriya, wanda zai iya tallafa wa burin Nijeriya na samar da tattalin arziki mai darajar dala tiriliyan ɗaya.

Domin cimma tsarin kuɗi mai ƙarfi da juriya, Babban Bankin Nijeriya (CBN) bai gajiya ba wajen jagorantar shirin sake ƙarfafa jarin bankuna ta hanyar ganin bankuna sun ninninka jarin su. Tun a ranar 28 ga Maris, 2024, CBN ya sanar da shirin sake ƙarfafa jarin bankuna na tsawon shekaru biyu, wanda ya fara aiki daga 1 ga Afrilu, 2024. Shirin ya tanadi mafi ƙarancin jari na naira biliyan 500 ga bankunan kasuwanci masu lasisin kasa da kasa, naira biliyan 200 ga masu lasisin ƙasa baki ɗaya, da kuma naira biliyan 50 ga bankunan yankuna. Lokacin cika waɗannan sharuɗɗa na watanni 24 zai ƙare a ranar 31 ga Maris, 2026.

Fitowar manyan bankuna masu ƙarfi na daga cikin babbar ribar da ake sa ran samu daga wannan shiri.
Babban bankin, a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Olayemi Cardoso, na da ra’ayin cewa samun ci gaban tattalin arziki mai ɗorewa na buƙatar cikakken goyon baya daga tsarin kuɗi. Saboda haka, CBN na ƙoƙarin daidaita manufofin kuɗi da na kasafin kuɗi domin cimma hangen nesa na gwamnati na bunƙasar kasuwanci da kuma gina tattalin arziki mai darajar dala tiriliyan ɗaya.

A cewar Cardoso, babban burin jagorancin CBN shi ne kare tsarin kuɗin Nijeriya tare da tabbatar da ƙarfin sa da sahihancin sa a cikin gida da ƙasashen waje, ta hanyar ƙarfafa tsarin bin doka da ƙa’ida da kuma inganta tsarin kula da ƙoƙarin kauce wa barazanar cikas. Don cimma wannan buri, CBN ya sake jaddada ƙudurin sa na tabbatar da tsarin kuɗi mai gaskiya da juriya, ta hanyar tsaurara bin ƙa’idojin doka da inganta kula da haɗari a dukkan cibiyoyin kuɗin Nijeriya.

Tantance Ci Gaban Sake Ƙarfafa Jari

Kafin wa’adin ranar 31 ga Maris, Mataimakin Gwamnan CBN mai kula da Manufofin Tattalin Arziki, Dakta Muhammad Abdullahi, ya bayyana a ranar Alhamis, 15 ga Janairu, a wani taron Ƙungiyar Tattalin Arzikin Nijeriya (NESG) a Legas, cewa bankuna 20 sun riga sun cika sabbin sharuɗɗan jari.

A tuna cewa a taron ƙarshe na Kwamitin Manufofin Kuɗi (MPC) na shekarar 2025, Cardoso ya bayyana cewa bankuna 16 sun riga sun cika dukkan sharuɗɗan sabbin ƙa’idojin jari kafin wa’adin ƙarshe. Bayanin Abdullahi ya nuna ci gaba mai kyau a ƙoƙarin CBN ƙarƙashin jagorancin Cardoso na kafa tsarin banki mai ƙarfi da juriya a ƙasar.

A halin yanzu, Nijeriya na da bankuna 44 masu karɓar ajiya a rukunoni daban-daban na lasisi. Yayin da wa’adin ke ƙaratowa, wakilin mu ya ji cewa aƙalla bankuna bakwai na duba yiwuwar rage lasisin su daga na ƙasa baki ɗaya zuwa na yankuna, la’akari da inda ayyukan su suka fi mayar da hankali da kuma irin damar da fasahar bankin zamani ta dijital ke bayarwa a faɗin ƙasar.

Haka kuma, an gano cewa wani banki mai lasisin ƙasa da ƙasa ya nuna a ‘yan kwanakin nan cewa yana iya rage lasisin sa zuwa na ƙasa baki ɗaya kafin wa’adin ƙarshe, yayin da yake ci gaba da ƙoƙarin ƙara jarin sa domin sake samun lasisin ƙasa da ƙasa.

CBN na rarraba bankuna zuwa rukuni uku – na kasa da kasa, na ƙasa baki ɗaya, da na yankuna – bisa ƙarfin su na kuɗi. A ƙarƙashin ƙa’idojin sake ƙarfafa jari, baya ga tara kuɗi, dole ne bankuna su gabatar da sabbin kuɗaɗen jarin su domin tantancewa kafin a amince da rabon hannun jari da sakin kuɗin don kammala aikin tayin da ƙara sabon jari a asusun jarin bankin.
CBN ne ke da sa hannun ƙarshe a kwamitin tantance jarin bankuna mai mambobi uku, wanda ya haɗa da Hukumar Kula da Kasuwar Hannun Jari (SEC) da Hukumar Kula da Inshorar Ajiya ta Nijeriya (NDIC). Aikin kwamitin shi ne duba da tantance sabbin kuɗaɗen da bankuna ke tarawa a ƙarƙashin shirin sake ƙarfafa jarin bankuna.

Sabon Jari Zai Kai Naira Tiriliyan 4.14

A cikin wani rahoto mai taken “Kalubalen Tattalin Arziki na Nijeriya Sun Haifar da Sake Ƙarfafa Jarin Bankuna”, kamfanin Deloitte ya kiyasta cewa jimillar kuɗin da za a tara a wannan shiri zai kai naira tiriliyan 4.14.

Rahoton ya ce ƙara mafi ƙarancin jarin bankuna daga naira biliyan 50 zuwa naira biliyan 500, gwargwadon nau’in lasisi, mataki ne mai matuƙar muhimmanci domin ƙarfafa isasshen jari a ɓangaren kuɗin Nijeriya. Rahoton ya kuma bayyana cewa isasshen jarin bankunan Nijeriya ya samu tasiri sosai daga kalubalen tattalin arziki kamar hauhawar farashi da ribar banki, sauyin darajar kuɗi, da ƙarancin musayar kuɗaɗen waje.

“Ƙarin jarin zai tabbatar da cewa bankunan Nijeriya na da ikon ɗaukar manyan ƙalubale da kuma tsayawa daram a lokacin girgizar tattalin arziki ta cikin gida da ta waje. Hakan kuma zai ƙara yawan kuɗin da ke hannun bankuna, wanda zai faɗaɗa ikon su na ɗaukar asara,” inji rahoton.

Yayin da ake sa ran tara sabon jari na naira tiriliyan 4.14, kuma bankuna 20 sun riga sun cika mafi ƙarancin sharuɗɗan jari, ana sa ran wannan shekara za ta zama muhimmin mataki a tattalin arzikin ƙasa.

A sabuwar sanarwar sa kan shirin sake ƙarfafa jari a watan Disambar 2025, Cardoso ya bayyana cewa CBN zai tsaurara tsarin shugabanci nagari, ƙara gaskiya, da ƙarfafa ɗaukar alhaki domin kare kuɗaɗen da aka tara. Ya kuma ce yayin da wasu bankuna sun riga sun cika sabbin sharuɗɗan jari, sauran suna samun ci gaba sosai kuma suna da kwarin gwiwar cika sharuɗɗan kafin ranar 31 ga Maris, 2026.

“Bankunan da suka cika ko suka wuce sabbin sharuɗɗa hujja ce bayyananniya ta zurfi, juriya, da ƙarfín tsarin bankin Nijeriya,” cewar Cardoso.

Tags: CBNOlayemi Cardoso
Previous Post

Gyaran tsarin ilimi na Tinubu yana samar da damarmaki ga matasan Nijeriya – Minista

Next Post

Haƙurin addini shi ne jigon zaman lafiya da haɗin kan Nijeriya – Tinubu

Related Posts

Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa

May 3, 2026
Tinubu zai fara rangadin tsawon mako biyu zuwa Faransa, Kenya da Ruwanda
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu zai fara rangadin tsawon mako biyu zuwa Faransa, Kenya da Ruwanda

May 1, 2026
Himma dai CBN: Tinubu ya sheƙa wa Cardoso ruwan jinjina da yabo kan nasarorin sauye-sauyen tsarin kuɗi da shirin ƙara jarin bankuna
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Himma dai CBN: Tinubu ya sheƙa wa Cardoso ruwan jinjina da yabo kan nasarorin sauye-sauyen tsarin kuɗi da shirin ƙara jarin bankuna

May 1, 2026
Cikar wa’adin ƙarfafa jari: Yadda bankunan Nijeriya suka bazama tara Naira tiriliyan 4.6 a ƙoƙarin cika sharuɗɗan CBN
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Juyin Zamani: Yadda CBN ke ƙarfafa wa ɗalibai koyon ilmin sarrafa kuɗi, yayin da tattalin arziki ke sauyawa a zamanance 

April 30, 2026
Yadda asusun kuɗaɗen waje na Nijeriya zai cika maƙil, bayan CBN ya yi wa naira allurar ƙarin ƙarfin wujijjiga dala a tsakiyar kasuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda CBN ke ta ƙoƙarin daƙile malejin hauhawar farashi zuwa ƙasa da kashi 10 bisa 100

April 29, 2026
Gargaɗi, sharuɗɗa da wa’adin da CBN ya gindaya kan BVN don tsaurara matakan tsare kuɗaɗen kwastomomi a bankuna
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Gargaɗi, sharuɗɗa da wa’adin da CBN ya gindaya kan BVN don tsaurara matakan tsare kuɗaɗen kwastomomi a bankuna

April 27, 2026
Next Post
Tsaro: Tinubu ya kira taron Majalisar Ƙoli ta ƙasa da ta ‘yan sanda

Haƙurin addini shi ne jigon zaman lafiya da haɗin kan Nijeriya – Tinubu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!