Gwamnatin Tarayya ta fara aikin samar da wutar lantarki daga hasken rana a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano.
Shugaban Hukumar Kula da Harkokin Makamashi ta Ƙasa (ECN), Dakta Mustapha Abdullahi, ya ce wutar lantarkin mai ƙarfin Megawatt huɗu (4MW) za ta bai asibitin damar rabuwa da layin wutar lantarki na ƙasa baki ɗaya.
Abdullahi ya ce aikin na daga cikin manufofin Shirin Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.
Ya bayyana cewa wannan tsari zai kawo ƙarshen matsalar yawan yanke wuta a asibitin, lamarin da a baya ya haddasa asarar rayukan marasa lafiya guda uku a lokacin da ayyukan asibitin suka tsaya cak.
“Da wannan tsari, ba za a sake samun irin waɗannan matsaloli ba. Burin mu shi ne mu samar da makamashi mai tsafta da nagarta wanda zai ƙarfafa cibiyoyin kiwon lafiya tare da inganta rayuwar ’yan Najeriya,” inji shi.







