• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Gwamna Raɗɗa ya rattaba hannu kan ƙudirin kasafin kuɗi na 2026 na N897.8 biliyan

Abbas Bamalli by Abbas Bamalli
November 26, 2025
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Gwamna Raɗɗa ya rattaba hannu kan ƙudirin kasafin kuɗi na 2026 na N897.8 biliyan
Gwamna Dikko Umar Raɗɗa na Jihar Katsina

Gwamna Dikko Umar Raɗɗa na Jihar Katsina

Gwamna Dikko Umar Raɗɗa na Jihar Katsina, a yau Laraba, ya rattaba hannu kan ƙudirin kasafin kuɗin jihar na 2026 mai darajar N897.8 biliyan, yana mai mai da shi doka.

An rattaba hannun ƙudirin ne a Fadar Gwamnatin Katsina, kuma an sanya masa taken ‘Gina Makomar Ku 3’.

Gwamnan ya yaba wa Majalisar Dokokin jihar bisa amincewa da kasafin cikin kwanaki 21 kacal na aiki.

Raɗɗa ya ce kasafin kuɗin, wanda ya ƙunshi kashi 18 cikin ɗari na kuɗin gudanarwa da kashi 81 cikin ɗari na kuɗin raya ƙasa, yana daga cikin gadon marigayi Shugaba Umaru Musa Yar’Adua.

Ya ce sabon kasafin, wanda ya rage yawan kuɗin gudanarwa, ya yi daidai da tsarin marigayi shugaban, wanda shi ma tsohon gwamnan jihar ne.

Gwamnan ya gode wa ’yan majalisar bisa sadaukar da lokacin su, har da barin hutu da yin daren rashin barci domin tabbatar da an wuce da kasafin, tare da yawan ƙudirorin da suka yi aiki a kan su a ’yan shekarun nan.

Raɗɗa ya jaddada muhimmancin kyakkyawar alaƙa tsakanin ɓangaren zartarwa da Majalisar Dokoki, tare da kira da a ci gaba da yin aiki tare.

Tun da farko, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar, Alhaji Nasir Yahya Daura, ya ce kasafin ya fito ne daga tsari mai zurfi da cikakken nazari, wanda ya haɗa da bincike da tambayoyi domin tabbatar da biyan buƙatun jama’a da cigaban jihar.

Ya tuna da cewa kasafin da ɓangaren zartarwa ya gabatar shi ne iri ɗaya da wanda aka amince da shi, wanda hakan ya sa majalisar ta yanke shawarar barin adadin kasafin yadda aka gabatar.

“Bayan nazari mai zurfi, majalisar ta gamsu cewa ƙudirin ya dace kuma yana tafiya da tsarin cigaban wannan gwamnati,” inji shi.

Kakakin ya roƙi taimakon Ubangiji wajen aiwatar da kasafin cikin nasara da kuma shawo kan matsalolin tsaro. (NAN)

Tags: Gwamna Dikko Umar RaɗɗaJihar KatsinaKasafin KuɗiMajalisar DokokiNasir Yahya Daura
Previous Post

CBN zai haramta wa ‘yan gidoga masu rubuta cek na bogi yin hulɗa da banki tsawon shekara biyar

Next Post

Tinubu ya naɗa sabbin jakadu zuwa Amurka, Birtaniya da Faransa

Related Posts

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

May 12, 2026
Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis

May 12, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Ƙwaƙudumar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba

May 8, 2026
Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya

May 7, 2026
Manyan nasarorin da CBN ya samu cikin 2025
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda ƙarfin laƙani da dafa’in CBN ke hana girgizar tattalin arzikin duniya yi wa Nijeriya barazana

May 6, 2026
Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris

May 5, 2026
Next Post
Tinubu ya naɗa sabbin jakadu zuwa Amurka, Birtaniya da Faransa

Tinubu ya naɗa sabbin jakadu zuwa Amurka, Birtaniya da Faransa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!