• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis

ASHAFA MURNAI BARKIYA by ASHAFA MURNAI BARKIYA
May 12, 2026
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis
Ana yi wa Lamiɗo Yuguda marhabin da shiga ofis

Ana yi wa Lamiɗo Yuguda marhabin da shiga ofis

Sabon Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Lamiɗo Yuguda, ya shiga ofis domin kama aiki a ranar Litinin, 11 ga Mayu, 2026.

Yuguda wanda Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya naɗa a ranar 11 Maris 2026, ya samu tarba daga manyan shugabannin CBN, ciki har da Gwamnan CBN, Olayemi Cardoso.

Tun a cikin watan Afrilu ne dai Majalisar Dattawa ta amince da naɗin wanda Shugaba Tinubu ya yi wa Yuguda.

An yi wannan naɗi ne bisa ƙa’idar da Sashe na 8(1) na Dokar Babban Bankin Nijeriya ta shekarar 2007 ta gindaya.

Naɗin Yuguda ya biyo bayan naɗa tsohon Mataimakin Gwamnan CBN, Mista Bala Bello, a matsayin Mai Bai wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tattalin Arzikin Siyasa.

Lamiɗo Yuguda

Shugaban Ƙasar ya buƙace su da su gudanar da ayyukan su da ƙarin jajircewa, ƙwarewa da sadaukarwa domin tabbatar da daidaiton tattalin arzikin Nijeriya da bunƙasar sa a mabambantan matsayin da aka naɗa su.

Lamiɗo Yuguda ya taɓa riƙe muƙamin Darakta Janar na Hukumar Kula da Kasuwar Hannayen Jari ta Ƙasa (SEC), muƙamin da ya riƙe daga shekarar 2020 zuwa 2024.

Mamba ne na ƙungiyar ƙwararrun masu bin-diddigin lissafi ta ICAN.

Ya fara aikin sa a shekarar 1984 a Babban Bankin Nijeriya (CBN) a matsayin Babban Mai Kulawa a Sashen Harkokin Kuɗaɗen Waje.

Haka kuma ya yi aiki a matsayin masanin tattalin arziki a Sashen Afrika na Asusun Bada Lamuni na Duniya (IMF), daga shekarar 1997 zuwa 2001, kafin ya koma CBN.

Ya yi ritaya daga CBN a shekarar 2016 bayan ya shafe shekaru shida a matsayin Daraktan Sashen Kula da Ajiyar Kuɗaɗe.

Tags: CBNLamiɗo Yugudanaɗi
Previous Post

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

Next Post

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

Related Posts

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

May 12, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Ƙwaƙudumar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba

May 8, 2026
Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya

May 7, 2026
Manyan nasarorin da CBN ya samu cikin 2025
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda ƙarfin laƙani da dafa’in CBN ke hana girgizar tattalin arzikin duniya yi wa Nijeriya barazana

May 6, 2026
Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris

May 5, 2026
Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa

May 3, 2026
Next Post
Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: "A kiyaye bin ƙa'idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!