• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris

Wakilin Mu by Wakilin Mu
May 5, 2026
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris
Shugaba Bola Ahmed Tinubu tare da manyan masu zuba jari na duniya a birnin Paris na ƙasar Faransa a yau 

Shugaba Bola Ahmed Tinubu tare da manyan masu zuba jari na duniya a birnin Paris na ƙasar Faransa a yau 

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a birnin Paris na ƙasar Faransa, inda ya jaddada aniyar gwamnatin sa na tabbatar da gaskiya, adalci, da kuma kiyaye ka’idojin kashe kuɗi. Shugaban ya kuma bayyana dalilan da suka sa aka aiwatar da garambawul ga tattalin arziki cikin gaggawa.

A yayin taron, Ministan Kuɗi da Tattalin Arziki, Taiwo Oyedele, ya bayyana nasarorin da Nijeriya ta samu, inda ya ce tattalin arzikin ƙasar ya haɓaka da kashi 11.2% (idan aka lissafa da dalar Amurka) a shekarar 2025.

A cewar sa, wannan ci gaba ya nuna cewa burin Nijeriya na ganin tattalin arzikin ta ya kai darajar dala tiriliyan ɗaya nan da shekarar 2030 zai iya tabbata. Oyedele ya kuma lashi takobin cewa gwamnati za ta riƙa wallafa bayanan kuɗi na kowane bayan watanni uku domin tabbatar da gaskiya.

Muhimman Abubuwan Da Aka Tattauna:

• Bashin Ƙasa: Shugabar Ofishin Kula da Basussuka (DMO), Patience Oniha, ta tabbatar wa masu zuba jarin cewa gwamnati tana amfani da bashi ta hanyar da ta dace kuma za ta tabbatar ba a jefa ƙasar cikin halin kaka-ni-ka-yi ba.

• Tsaro da Man Fetur: Tinubu ya bayyana cewa gwamnati na ƙoƙarin gyara harkar mai don daina tafka asara, sannan ana shirin rarraba ikon rundunar ‘yan sanda (decentralisation) don magance matsalar tsaro da kuma toshe hanyoyin samar wa ‘yan ta’adda kuɗi.

• Makomar 2027: Lokacin da aka tambaye shi game da shirin sa na bayan shekarar 2027, Shugaban ya yi alƙawarin ci gaba da ƙarfafa tsarin tattalin arziki da tabbatar da cewa ba a canza manufofin da aka sa gaba ba.

Taron ya samu halartar wakilai daga manyan kamfanoni na duniya, ciki har da:

1. Citibank da Amundi (Faransa) karkashin jagorancin Valerie Baudson.
2. BlueCrest da Ninety One (Birtaniya da Afrika ta Kudu).
3. Kirkoswald Capital, Principal Finisterre, da PGIM (Amurka).

Masu zuba jarin sun yaba da matakan gyara da Shugaba Tinubu ya ɗauka, inda suka nuna kyakkyawan fata kan makomar tattalin arzikin Nijeriya.

Previous Post

Tinubu ya taya Garo murnar zama mataimakin gwamnan Kano

Next Post

ICPC ta ƙalubalanci sabuwar buƙatar beli da El-Rufai ya gabatar yayin da kotu ta ɗage sauraron ƙarar zuwa 13 ga Mayu

Related Posts

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

May 12, 2026
Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis

May 12, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Ƙwaƙudumar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba

May 8, 2026
Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya

May 7, 2026
Manyan nasarorin da CBN ya samu cikin 2025
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda ƙarfin laƙani da dafa’in CBN ke hana girgizar tattalin arzikin duniya yi wa Nijeriya barazana

May 6, 2026
Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shirin daƙile harƙalla: Yadda CBN ke amfani da sashen bankaɗo kuɗaɗen da ake karkatarwa

May 3, 2026
Next Post
ICPC ta ƙalubalanci sabuwar buƙatar beli da El-Rufai ya gabatar yayin da kotu ta ɗage sauraron ƙarar zuwa 13 ga Mayu

ICPC ta ƙalubalanci sabuwar buƙatar beli da El-Rufai ya gabatar yayin da kotu ta ɗage sauraron ƙarar zuwa 13 ga Mayu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!