• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Cewar Ministan Yaɗa Labarai: Tawagar da Gwamnatin Tarayya ta tura zuwa Amurka tana samun nasarar magance labaran ƙarya game da yanayin tsaron Nijeriya

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
November 22, 2025
in Labarai
A A
0
Gwamnatin Tarayya Ta Jajanta Wa Jihar Neja Bisa Fashewar Tankar Mai a Essa
Alhaji Mohammed Idris, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai

Alhaji Mohammed Idris, Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa tawagar manyan jami’an Gwamnatin Tarayya da ta tafi ƙasar Amurka a ƙarƙashin jagorancin Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Malam Nuhu Ribaɗu, tana gudanar da aiki sosai wajen magance labaran da ake yaɗawa na ƙarya da ke nuna wai ana cin zarafin addinai a Nijeriya.

“Ba mu bar sarari ga yaɗa bayanan karya ba. Jami’an mu suna Washington da hujjoji, bayanai, da saƙo a fili cewa babu wani cin zarafi ko danniya da gwamnati ke yi wa kowace ƙungiyar addini a Nijeriya,” inji Idris a wata hira da aka yi da shi a Politics Today na gidan talbijin na Channels, wadda aka watsa a yammacin Asabar.

Ministan ya bayyana cewa tawagar manyan jami’an Nijeriya da ke Amurka sun gana da Sakataren Yaƙi na Amurka, membobin Majalisar Dokokin Amurka, jami’an Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, da sauran muhimman shugabannin ƙasar, inda suka gabatar da hujjojin gaskiya game da ƙalubalen tsaron Nijeriya, tare da yin cikakken bayani kan yaƙi da ta’addanci, haɗin gwiwar hukumomin tsaro, da ƙoƙarin kare ’yan Nijeriya ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.

A cewar Ministan, waɗannan tattaunawar suna da matuƙar muhimmanci wajen gyara ra’ayoyin da aka yi wa ƙarin gishiri a cikin tattaunawar majalisa da yaƙin neman goyon bayan ƙungiyoyi na baya-bayan nan.

Ya ce: “Manufar mu a bayyane take… Muna nuna wa abokan hulɗar mu cikakken bayani game da halin tsaro, matakan da gwamnati ke ɗauka, da kuma cewa ’yan ta’adda sun kashe Kiristoci da Musulmi. Labaran da ake yaɗawa na kisan ƙare dangi ba daidai ba ne, kuma suna da haɗari.”

Ministan ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana ɗaukar wannan lamari da matuƙar muhimmanci, inda ba kawai ya ƙarfafa tsarin tsaro na cikin gida ba, har ma ya faɗaɗa haɗin kai da ƙasashen duniya domin tallafa wa yaƙi da ta’addanci da harkokin leƙen asiri.

Ya ce aikace-aikacen da tawagar ke yi na nuna ƙudirin gwamnatin Shugaba Tinubu na kare martabar Nijeriya da tabbatar da cewa abokan hulɗa na ƙasashen waje suna yanke shawara bisa bayanan da aka tantance, ba kan labaran gefe guda ba.

Ya jaddada cewa dangantakar Nijeriya da Amurka tana ƙarfi, kuma waɗannan mu’amalar suna nuna buɗaɗɗen salon gwamnatin Tinubu na tattaunawa, haɗin kai, da fayyace gaskiya.

Ya kuma bayyana cewa ana sa ran gudanar da ƙarin tarurruka a kwanaki masu zuwa a matsayin wani ɓangare na tsare-tsaren gwamnati na kare gaskiya a game da haƙiƙanin halin tsaron Nijeriya.

Idris ya buƙaci ’yan Nijeriya da su kwantar da hankalin su, tare da tabbatar wa da jama’a cewa gwamnati za ta ci gaba da yaƙi da rashin tsaro, tare da ci gaba da hulɗa da ƙasashen duniya don tabbatar da cewa a fagen duniya ana gabatar da sahihin labari a kan Nijeriya.

Tags: Amurkalabaran ƙaryaMohammed IdrisNuhu Ribadutsaro
Previous Post

Nijeriya ta nemi ƙarin haɗin gwiwar kafofin yaɗa labarai na ƙasashen D-8, ta lissafa sauye-sauyen da take samu a gida

Next Post

Hukuncin da aka yanke wa Nnamdi Kanu ya ƙara dagula matsalolin Nijeriya, inji Peter Obi

Related Posts

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500
Labarai

EFCC ta kama Darakta Janar na Hukumar Makamashi ta Nijeriya, Mustapha Abdullahi, kan zargin zambar naira biliyan 500

May 13, 2026
Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Next Post
Hukuncin da aka yanke wa Nnamdi Kanu ya ƙara dagula matsalolin Nijeriya, inji Peter Obi

Hukuncin da aka yanke wa Nnamdi Kanu ya ƙara dagula matsalolin Nijeriya, inji Peter Obi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!