Kakakin Majalisar Tarayya, Tajuddeen Abbas, ya bayyana fargaba dangane da ɗimbin bashin da ake bin Nijeriya, yana mai gargaɗi cewa yawan bashin ya zarce adadin dokar ƙasa ta gindaya ciwowa fintinkau.
Ya ce a yanzu haka yawan bashin da yawan kuɗaɗen ruwan da ake biya na yin barazana ga kuɗaɗen shiga da waɗanda gwamnati ke kashewa wajen gudanar da ayyukan yau da kullum na wajibi, har ma ga ɗorewar tattalin arziki.
Da yake jawabi a yau Litinin yayin buɗe taron shekara-shekara na 11, na Majalisar Kwamiti-kwamitin Masu Sa-ido Kan Harkokin Kuɗaɗe na Majalisun Ƙasashen Afrika ta Yamma (WAAPAC) a Majalisar Ƙasa, a Abuja, Abbas ya ce bashin da ake bin Nijeriya “ya kai maƙurar barazana.'”
Ya yi kira a gaggauta kawo sauye-sauye wajen gyara tsari da ƙa’udojin ciwo basussuka, sannan kuma majalisa ta riƙa sa-ido kan ayyukan da gwamnati ke aiwatarwa.
Ya ce: “Zuwa ƙarshen watanni uku na farkon 2025, adadin bashin da ake bin Nijeriya ya kai Naira tiriliyan 149.39, kwatankwacin kusan Dala biliyan 97. Hakan kuwa ya nuna cewa adadin ya ƙaru daga Naira tiriliyan 121.7 da ake bin Nijeriya a 2024”.
Ya ƙara da cewa, “Wani ƙarin abin damuwa shi ne idan aka ɗora adadin bashin bisa sikelin ƙarfin tattalin arziki na cikin gida, za a ga ya haura ƙa’idar adadin da doka ta ce a ciwo bashi ya kai kusan kashi 52 bisa 100.
“Domin dokar mu cewa ta yi kada fa bashin da aka ciwo ya haura kashi 40 bisa 100 na ƙarfin tattalin arzikin cikin gida, wanda dokar mu ta ce kada ya wuce haka.”
Ya ce saboda haka wannan abin damuwa ne matuƙar gaske. Sai ya yi kira a samar da sababbin ƙa’idoji kuma a riƙa sa-ido.
“Ya kamata kuɗaɗen da ake ciwowa bashi a riƙa ganin alfanun su ƙuru-ƙuru a fannin ayyukan raya ƙasa, kiwon lafiya, inganta ilmi da kuma masana’antu domin a samu ayyuka, sannan a rage fatara, talauci da raɗaɗin tsadar rayuwa.
“Amma yawan ciwo basussukan da ba su haifar da komai sai cin hanci da rashawa, dole ne fa a riƙa fallasa su, kuma ana bijire wa amincewa a ciwo shi,” inji shi.







