• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Siyasa

Dalilin mu na sanya ranakun Zaɓen 2027 a watan Ramadan, amma mun lura da damuwar jama’a – INEC

Fati Abdul by Fati Abdul
February 15, 2026
in Siyasa
A A
0
Dalilin mu na sanya ranakun Zaɓen 2027 a watan Ramadan, amma mun lura da damuwar jama’a – INEC
INEC

INEC

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa Mai Zaman Kan ta (INEC) ta yi tsokaci kan damuwar jama’a da ta taso bayan fitar da Jadawalin Lokuta da Tsarin Ayyuka na Babban Zaɓen 2027, musamman dangane da ranakun da aka ƙayyade domin gudanar da zaɓukan.

A cikin wata sanarwa da Mohammed Kudu Haruna, Kwamishinan Ƙasa kuma Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai da Wayar da Kan Masu Zaɓe, ya sanya wa hannu, hukumar ta tunatar da jama’a cewa ta tsara jadawalin ne bisa cikakken bin ƙa’idojin lokutan da ke cikin Tsarin Mulkin Nijeriya, da Dokar Zaɓe, da kuma Dokoki da Ƙa’idojin INEC na Gudanar da Zaɓe na 2022.

Ya ce Dokoki da Ka’idojin INEC na Gudanar da Zaɓe, da aka zartar tun a 2019, sun ƙayyade ranakun da za a riƙa gudanar da zaɓe.

Sashi na 2 na dokar ya tanadi cewa: “Zaɓen Shugaban Ƙasa da Mataimakin sa, da kuma na Majalisar Dokoki ta Ƙasa, za a gudanar da su ne a ranar Asabar ta uku a watan Fabrairu na duk shekarar da za a yi Babban Zaɓe; yayin da zaɓen Gwamna da Mataimakin sa da na Majalisun Dokokin Jihohi za a gudanar da su makonni biyu (2) bayan haka.”

Dangane da haka, kuma bisa cikakken bin waɗannan dokoki da ƙa’idoji da ke aiki, hukumar ta sanya ranar Asabar, 20 ga Fabrairu, 2027 domin Zaɓen Shugaban Ƙasa da na Majalisar Dokoki ta Ƙasa, sannan Asabar, 6 ga Maris, 2027 domin Zaɓen Gwamnoni da na Majalisun Dokokin Jihohi.

Ya ce: “Duk da haka, hukumar ta lura da damuwar da masu ruwa da tsaki suka bayyana dangane da daidaituwar ranakun da aka tsara da wasu bukukuwa da lokutan ibada da ƙasa ta amince da su.

“Hukumar na son ta tabbatar wa jama’a cewa tana kulawa da duk wata halastacciyar damuwa da ka iya shafar fitowar jama’a kaɗa ƙuri’a da kuma yadda za a gudanar da zaɓe gaba ɗaya.”

Ya ƙara da cewa, “Dangane da waɗannan buƙatu da aka gabatar, hukumar na ci gaba da tattaunawa, kuma idan ya zama dole, za ta nemi matakin gyara ta fuskar doka domin magance damuwar da ta taso, tare da tabbatar da cewa duk wani sauyi ya yi daidai da tanade-tanaden kundin tsarin mulki da dokoki.”

INEC ta sake jaddada ƙudirin ta na tabbatar da gaskiya, haɗin kai da kuma gudanar da Babban Zaɓen 2027 cikin sahihanci.

Ya ce za a sanar da jama’a duk wani sabon cigaba da zarar an samu.

Tags: DokarZabeINECranakunzabezaben2027
Previous Post

Gobarar Kasuwar Singa: Tinubu ya tura tawaga ƙarƙashin Shettima domin yin jaje

Next Post

Tinubu zai kai ziyarar aiki a Yola, zai ƙaddamar da ayyukan gwamnati

Related Posts

An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Tinubu ya taya Garo murnar zama mataimakin gwamnan Kano
Siyasa

Tinubu ya taya Garo murnar zama mataimakin gwamnan Kano

May 5, 2026
Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Tinubu zai kai ziyarar aiki a Yola, zai ƙaddamar da ayyukan gwamnati

Tinubu zai kai ziyarar aiki a Yola, zai ƙaddamar da ayyukan gwamnati

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!