Shugaba Bola Tinubu zai kai ziyarar aiki ta yini guda zuwa Jihar Adamawa a ranar Litinin, ƙasa da awanni 48 bayan makamanciyar ziyarar da ya kai Jihar Kebbi.
A yayin ziyarar, Shugaban Ƙasar zai ƙaddamar da wasu muhimman ayyuka da aka kammala tare da ganawa da manyan jami’an gwamnati da kuma sarakunan gargajiya na jihar.
Daga cikin ayyukan da aka shirya ƙaddamarwar a birnin Yola da Jimeta akwai Titin Galadima Aminu mai layi takwas da ya haɗa Gimba da babban birnin jihar.
Haka kuma, zai ƙaddamar da makarantar zamani da ta ƙunshi matakan firamare, ƙananan makarantun gaba da firamare, da kuma ƙaramar sakandare.
Sauran ayyukan sun haɗa da sabon babban ɗakin taruka mai ɓangarori da dama, kotun ƙoli da aka sake gyarawa, sabon ginin gidajen jami’ai, da kuma gyaran Fadar Gwamnati.
Bayan kammala ƙaddamar da ayyukan da ganawar da zai yi da al’ummar jihar, Tinubu zai koma Abuja a ranar.







