• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Tinubu ya rantsar da Muttaqha Darma a matsayin Ministan Gidaje

Wakilin Mu by Wakilin Mu
April 24, 2026
in Labarai
A A
0
Tinubu ya rantsar da Muttaqha Darma a matsayin Ministan Gidaje
Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana musabaha da Dakta Muttaqha Rabe Darma wajen naɗin sa matsayin sabon Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane na Tarayya a Fadar Shugaban Ƙasa yau Juma'a a Abuja

Shugaba Bola Ahmed Tinubu yana musabaha da Dakta Muttaqha Rabe Darma wajen naɗin sa matsayin sabon Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane na Tarayya a Fadar Shugaban Ƙasa yau Juma'a a Abuja

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya rantsar da Dakta Muttaqha Rabe Darma a matsayin sabon Ministan Gidaje da Bunƙasa Birane na Tarayya a yau Juma’a.

Rantsar da Darma, wanda ɗan asalin Jihar Katsina ne, ya biyo bayan amincewa da takardar naɗin sa da Majalisar Dattawa ta yi. Ya maye gurbin Ahmed Musa Ɗangiwa wanda ya yi murabus kwanan nan.

A wani taƙaitaccen biki da aka gudanar a Fadar Shugaban Ƙasa, Tinubu ya taya sabon ministan murna, inda ya bayyana cewa ya zo ne a daidai lokacin da ƙasar nan ke fuskantar ƙalubalen neman cigaba.

Shugaban ya yaba wa Darma inda ya ce: “Kuna da ƙwarewa da kyakkyawan tarihin aiki. A matsayin mu na shugabanni, muna buƙatar ƙwararru irin ku. Babu shakka kun taka rawar gani a duk inda kuka yi aiki a baya, don haka kun dace da wannan matsayi.”

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tare da Dakta Muttaqha Rabe Darma bayan rantsarwar

Wanene Dakta Muttaqha Darma?

Dakta Darma babban masani ne kuma ƙwararren mai gudanarwa wanda ya yi karatun digiri na uku a fannin harkar kasuwanci daga Jami’ar Liverpool, da kuma wani digiri na ukun a fannin “Industrial Engineering” daga Amurka.

Tarihin sa na karatu da aiki ya hada da:

• Digiri na farko a fannin “Mechanical Engineering” daga Jami’ar Bayero ta Kano (BUK).

• Ya taɓa zama Sakataren Gudanarwa na Asusun Tallafa wa Fasahar Man Fetur (PTDF) daga 2008 zuwa 2012.

• Ya riƙe muƙaman Kwamishinan Ayyuka da Gidaje, da kuma Kwamishinan Matasa da Walwalar Jama’a a Jihar Katsina.

• Ya taɓa zama malami a Jami’ar Bayero ta Kano.

Kafin wannan naɗe-naɗen, Darma shi ne Shugaban Cibiyar Bunƙasa Ɗan’adam ta Umaru Musa Yar’Adua da ke Katsina.

Sabon ministan ya sha alwashin yin amfani da ƙwarewar sa domin tabbatar da cewa an samar wa ‘yan Nijeriya gidaje masu rahusa da kuma inganta biranen ƙasar nan kamar yadda tsarin gwamnati mai ci ya tanada.

Tags: Ministan GidajeMuttaqha Rabe DarmanaɗiTinubu
Previous Post

Me ya sa har yanzu ake ciwo bashi bayan Tinubu ya cire tallafin mai? – Sarki Sanusi

Next Post

Gwamnatin Tarayya ta samar da tsarin rage kudin sufuri ta kan ba da lamunin sauya injinan mota zuwa na CNG

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya
Labarai

Ranar ’Yancin ’Yan Jarida ta Duniya: Nijeriya na neman a haɗa gwiwa a yaƙi masu yaɗa labaran ƙarya

May 4, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja
Labarai

Shettima ya ƙaddamar da jigilar maniyyatan Hajjin bana da kwashe alhazai 500 a Abuja

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Next Post
Gwamnatin Tarayya ta samar da tsarin rage kudin sufuri ta kan ba da lamunin sauya injinan mota zuwa na CNG

Gwamnatin Tarayya ta samar da tsarin rage kudin sufuri ta kan ba da lamunin sauya injinan mota zuwa na CNG

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!