Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed (Ƙaura), ya nuna yiwuwar ficewar sa daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP), inda ya bayyana African Democratic Congress (ADC) a matsayin dandalin siyasar da ya fi so, sakamakon tsananin rikicin cikin gida da ke ƙara ƙamari a cikin jam’iyyar su ta adawa.
Gwamnan, wanda kuma shi ne Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin PDP, ya bayyana hakan ne a yau Talata yayin da yake karɓar wata babbar tawaga ta ADC a Fadar Gwamnati da ke Bauchi.
Tawagar tana ƙarƙashin jagorancin tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya, Mista Babachir Lawal, waɗanda suka je bisa umurnin shugabannin jam’iyyar na ƙasa.
Da yake zantawa da ‘yan jarida bayan ganawar sirri da suka yi, Bala Mohammed ya koka kan yadda rarrabuwar kai take ƙara tsananta a cikin PDP, yana mai bayyana cewa ƙoƙarin sasanta ɓangarorin da ke rikicin ya ci tura.
Ya ce: “Mun tsinci kan mu a cikin wani yanayi mai matuƙar tsanani. Na yi duk mai yiwuwa domin ganin an samu sulhu, amma hakan bai yi nasara ba.”
Gwamnan ya ƙara da cewa an kafa kwamitoci a matakin ƙasa da jiha domin nemo mafita, ciki har da tuntubar wasu jam’iyyun siyasa.
Sai dai ya ce har ma yunƙurin tuntuɓar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulkin ƙasa bai haifar da ɗa mai ido ba.
Ya bayyana ƙoƙarin da ya yi na shiga APC amma aka ƙi karɓar sa, ya ce, “Mun gwada shiga dukkan jam’iyyu, har da APC, amma abin takaici mun gano cewa ba a son mu a can.”
A wannan yanayi, Bala ya ce ADC ita ce ta fi nuna maraba da shi kuma ta zama zaɓin da ya fi dacewa da shi a halin yanzu.
“A yanzu, ADC na bayyana a matsayin dandalin da ke karɓar mu kuma mafi dacewa. Duk da haka, ba mu kammala tattaunawa ba. Muna ci gaba da tuntuɓar masu ruwa da tsaki domin kauce wa yin kuskure.”
Gwamnan ya nuna cewa tuntuɓa ta ƙarshe na ci gaba kuma sun kusa kammalawa, inda ake sa ran yanke hukunci nan ba da jimawa ba.
Ya ce: “Muna sane da muhimmancin lokaci. Za a kammala komai kafin ranar Alhamis domin mu ci gaba tare. Za ku ji cikakken matsayar mu.”
Bala ya kuma zargi cewa rikicin da ke addabar PDP yana ƙara tsananta ne sakamakon tsoma baki sa wasu ke yi daga waje, musamman yana zargin Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da zama kanwa-uwar-gami a rikicin.
A cewar sa, irin waɗannan tasiri sun sa ƙoƙarin sulhu ya ƙara wahala tare da zurfafa rarrabuwar kai a cikin jam’iyyar.
Ya kuma bayyana cewa ya yi ganawar musamman da manyan ‘yan siyasa, ciki har da shugabannin APC da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, domin warware matsalar, amma hakan bai samar da mafita mai ɗorewa ba.
Tun da farko, Babachir Lawal ya ce ziyarar tawagar ADC ɗin wani ɓangare ne na dabarun haɗa kan jam’iyyun adawa gabanin zaɓen shekarar 2027.
Ya bayyana cewa wannan yunƙuri ya samo asali ne daga shugabancin jam’iyyar ƙarƙashin tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, domin ƙarfafa ADC a matsayin ingantaccen zaɓin dandalin siyasa.
Ya ce: “Ceton Nijeriya a 2027 yana buƙatar haɗin kan dukkan ‘yan Nijeriya masu kishin ƙasa. Mun zo ne domin tattaunawa da Gwamna Bala Mohammed saboda ƙwarewar sa da gogewar sa a siyasa.”
Ya bayyana fatan cewa tattaunawar da ake yi za ta haifar da sakamako mai kyau, yana mai cewa a shirye ADC take ta karɓi gwamnan da magoya bayan sa.







