• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Wednesday, May 13, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Ministan Yaɗa Labarai ya taya Tinubu murnar cika shekara 74

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
March 29, 2026
in Labarai
A A
0
Ministan Yaɗa Labarai ya taya Tinubu murnar cika shekara 74
Shugaba Tinubu ya cika shekaru 74 a yau

Shugaba Tinubu ya cika shekaru 74 a yau

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya taya Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu murnar cika shekara 74, yana mai bayyana shi a matsayin jagora wanda salon jagorancin sa da gyare-gyaren sa suke ci gaba da tasiri wajen bunƙasa Nijeriya.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, Idris ya ce wannan lokaci ne na tuna irin gudunmawar da Shugaban Ƙasar yake bayarwa wajen cigaban ƙasa da kuma jajircewar sa wajen kawo sauye-sauye masu ma’ana.

Ya ce: “Wannan lokaci ne na murnar jagora wanda jarumtaka da hangen nesan sa suke ci gaba da jagorantar Nijeriya a wannan lokaci na gyare-gyare da farfaɗowar ƙasa.”

Ministan ya ƙara da cewa shirin Shugaban Ƙasa Tinubu na ɗaukar matakai masu wahala sun sanya ƙasar nan kan turbar bunƙasa da daidaito na dogon lokaci.

Ya kuma bayyana cewa mayar da hankali kan tsare gaskiya, sadarwar da ta dace da haɗin kan ƙasa na ci gaba da jagorantar ayyukan ma’aikatar.

Ya ce ƙarfafa sadarwa mai tsari da hulɗa da jama’a da kuma yaƙi da yaɗa bayanan ƙarya suna nuna muhimmancin gaskiya da amincewa a harkokin mulki.

Idris ya faɗa wa Shugaban Ƙasa: “A yayin da kake bikin wannan rana ta musamman, muna yaba maka bisa hidimar ka ga ƙasa da kuma jajircewar ka wajen gina Nijeriya mai amfani ga kowa.”

Ya kuma yi addu’ar Allah ya ƙara masa lafiya, ƙarfi da hikima wajen ci gaba da jagorantar ƙasar nan zuwa ga cigaba mai ɗorewa.

Tags: birthdayMohammed Idrisshekaru74Tinubu
Previous Post

Kwankwasiyya ta umurci mabiyan ta su shiga ADC, ta ce Kwankwaso zai yi rajista da jam’iyyar a gobe

Next Post

Hausa Zalla Ko Zallar Jahilci?

Related Posts

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista
Tsaro

Nijeriya ta sha alwashin sabunta rundunonin sojin ta ta hanyar haɗin gwiwa da bunƙasa ƙwarewar cikin gida – Minista

May 13, 2026
Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75
Labarai

Zambar naira biliyan 33.8: Kotu ta yanke wa tsohon Ministan Wutar Lantarki, Saleh Mamman, hukuncin ɗaurin shekaru 75

May 13, 2026
Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu
Ilimi

Za a riƙa yi wa ɗaliban makarantun sakandare gwajin tilas na ƙwayoyi daga yanzu

May 11, 2026
An kama Bello Boɗejo, shugaban Fulani Kuma ɗan takarar kujerar Sanata na APC a Taraba
Siyasa

An miƙa ɗan takarar Sanata kuma shugaban Fulani, Bello Boɗejo ga EFCC

May 10, 2026
Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka
Tsaro

Ribaɗu da JD Vance sun gana don ƙarfafa alaƙar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka

May 9, 2026
Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro
Tsaro

Dakaru sun aika da ’yan ta’adda masu yawa barzahu, sun ceto mutum 50, inji hedikwatar tsaro

May 9, 2026
Next Post
Hausa Zalla Ko Zallar Jahilci?

Hausa Zalla Ko Zallar Jahilci?

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!