Dakarun Nijeriya sun kashe ‘yan ta’adda 61 a Malam Fatori da ke da ke Ƙaramar Hukumar Abadam a Jihar Borno.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne yayin da ‘yan ta’addan suka yi ƙoƙarin kutsa kai cikin sansanin sojin da ke garin Malam Fatori.
Wani rahoton da Zagazola Makama ya fitar wanda babban mai bai wa Shugaba Tinubu shawara na musamman kan dabaru da watsa labarai, Bayo Onanuga, ya wallafa a shafin sa na X, ya ce lamarin ya auku ne a lokacin da ‘yan ta’addan suka nemi kutsawa cikin sansanin soji a Malam Fatori.
Rahoton ya ambato majiyoyin tsaro suna cewa ‘yan ta’addan sun ƙaddamar da harin da sanyin safiyar yau Laraba ne inda suka nufi sansanin sojin da ƙafa kuma suka yi amfani da jirage mara matuƙa a wani yunƙuri na karya katangar sansanin sojin da ƙarfin hali.
Sai dai martani mai ƙarfi na haɗin gwiwa da dakarun ƙasa da na sama suka yi ya fi ƙarfin ‘yan ta’addan.
Kazalika wata sanarwar da daraktan hulɗa da jama’a da watsa labarai na rundunar sojin saman Nijeriya, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya fitar kuma Usman Kukasheka, tsohon kakakin sojin Nijeriya ya wallafa a shafin sa na Facebook, ta tabbatar da aikin da sojin saman ta yi a Malam Fatori.
“Aikin na haɗin gwiwa ya yi nasarar hana masu tayar da ƙayar bayan karya katangun tsaro, lamarin da ya ƙarfafa ƙoƙarin da ake yi na daidaita lamurra a garuruwan da ke kan iyakoki,“ inji sanarwar.







