• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Ƙasashen Duniya

Ma’aikatan jirgi 4 sun mutu lokacin da jirgin ɗaukar mai na Sojin Saman Amurka ya faɗi a Iraƙi, inji sojoji

* Mu ne muka kakkaɓo shi, inji ƙungiyar gwagwarmayar Islama ta Iraƙi

ALI KANO by ALI KANO
March 13, 2026
in Ƙasashen Duniya
A A
0
Ma’aikatan jirgi 4 sun mutu lokacin da jirgin ɗaukar mai na Sojin Saman Amurka ya faɗi a Iraƙi, inji sojoji
Wani jirgin ɗaukar mai na Amurka samfurin KC-135 Stratotanker yana shawagi a sararin kudancin Japan a ranar 30 ga Agusta, 2023. (Hoto: AP)

Wani jirgin ɗaukar mai na Amurka samfurin KC-135 Stratotanker yana shawagi a sararin kudancin Japan a ranar 30 ga Agusta, 2023. (Hoto: AP)

Ma’aikatan jirgi huɗu sun mutu bayan wani jirgin ɗaukar mai na Sojin Sama na Amurka ya faɗi a Iraƙi ranar Alhamis, kamar yadda Babbar Rundunar Yaƙi ta Amurka (US Central Command) ta bayyana a safiyar Juma’a.

Jaridar New York Post ta ruwaito a gidan yanar ta yau Asabar cewa jirgin man na Amurka mai suna KC-135 Stratotanker yana ɗauke da ma’aikata shida a cikin sa lokacin da aka rasa shi a sararin samaniya na yankin da ake da alaƙar abota da su, a wani lamari da ya faru a daidai lokacin yaƙin da Amurka da Isra’ila suke kai wa Iran mai taken “Operation Epic Fury.”

“Har yanzu ana binciken yadda lamarin ya faru. Sai dai rasa jirgin bai faru sakamakon harbin abokan gaba ko kuma harbin kuskure daga abokan hulɗa ba,” inji sanarwar.

Jirage biyu ne dai suka shiga cikin lamarin, inda jirgi na biyu ya sauka lafiya.

Sojojin Amurka sun ce za su ɓoye sunayen ma’aikatan sojin da suka mutu har sai bayan awanni 24 bayan an sanar da iyalansu.

Sai dai kuma ƙungiyar gwagwarmayar mai suna Islamic Resistance in Iraq, wadda gangamin ƙungiyoyin mayaƙa ce masu samun goyon bayan Iran, ta ce ita ce ta harbo jirgin a yammacin ranar Alhamis.

A cikin wata sanarwa, ƙungiyar ta ce ta kakkaɓo jirgin ɗaukar mai ɗin na sojin ne “don kare ikon ƙasar mu da sararin samaniyar ta.”

Shi dai irin wannan jirgi, yakan ba jirgin sama mama ne (wato mai) a sararin samaniya ba tare da sun sauko ƙasa ba.

Tags: AmurkafaɗuwahaɗariIranIraƙiIsra'ilajirgimutuwastratotankeryaƙi
Previous Post

Kotu ta amince wa ICPC ta binciki na’urorin da aka ƙwato daga gidan El-Rufa’i

Next Post

Gwamnan CBN ya jaddada muhimmancin ƙarfafa cibiyoyi da gyaran jarin bankuna domin bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa

Related Posts

Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce
Ƙasashen Duniya

Netanyahu ya bayyana cewa ya yi jinyar cutar sankarar ‘ya’yan maraina a asirce

April 24, 2026
Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma
Ƙasashen Duniya

Isra’ila ta tabbatar da sahihancin hoton soja yana bugun gunkin Yesu da guduma

April 20, 2026
Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa
Ƙasashen Duniya

Ɗan bindiga a Amurka ya kashe yara 8, ciki har da 7 daga cikin ‘ya’yan sa

April 20, 2026
Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran
Ƙasashen Duniya

Za mu sake datse Mashigar Hormuz, inji Iran

April 18, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Ƙasashen Duniya

CBN na shirin kafa kwamitin sulhu don warware rikice-rikicen masu taurin bashi

April 17, 2026
Iran ta kakkaɓo jirgin yaƙin Amurka a sararin samaniyar ta
Ƙasashen Duniya

Iran ta kakkaɓo jirgin yaƙin Amurka a sararin samaniyar ta

April 3, 2026
Next Post
Gwamnan CBN ya jaddada muhimmancin ƙarfafa cibiyoyi da gyaran jarin bankuna domin bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa

Gwamnan CBN ya jaddada muhimmancin ƙarfafa cibiyoyi da gyaran jarin bankuna domin bunƙasar tattalin arziki mai ɗorewa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!