• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Thursday, May 14, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Kuɗi Da Tattalin Arziki

Ƙungiyar NFTD ta jinjina wa Yakubu, Babban Daraktan Ofishin Kasafin Kuɗaɗen Tarayya

ASHAFA MURNAI BARKIYA by ASHAFA MURNAI BARKIYA
October 26, 2025
in Kuɗi Da Tattalin Arziki
A A
0
Ƙungiyar NFTD ta jinjina wa Yakubu, Babban Daraktan Ofishin Kasafin Kuɗaɗen Tarayya
Dakta Tanimu Yakubu

Dakta Tanimu Yakubu

Ƙungiyar NFTD, mai rajin jaddada bin ƙa’ida da bayyana yadda ake kashe kuɗaɗen gwamnati, ta jinjina tare da nuna yabo ga Babban Daraktan Ofishin Kasafin Kuɗaɗen Tarayya, Tanimu Yakubu, dangane da yadda ya fito da tsarin fayyace yadda ake aiwatar da ayyukan kasafin kuɗi a fili.

NFTD ta kuma yaba ƙoƙarin Yakubu bisa yadda yake sa-ido sosai wajen yadda ake aiwatar da kasafin, tare da auna shi bisa gwargwadon ma’aunin da ya dace.

Cikin wata sanarwar da Babban Kodineta na Ƙasa na ƙungiyar, mai suna Joshua Oyenuga ya fitar a ranar Lahadi, mai ɗauke da sa hannun sa, ƙungiyar ta bayyana cewa, rahoton da Yakubu ya fitar kan yadda aka aiwatar da Kasafin 2024, “wani sabon babi ne sahihi a ƙasar nan kan yadda ake sa-ido wajen kashe kuɗaɗe a ɓangarorin ayyukan kasafi.”

NFTD ta ci gaba da cewa rahoton na Ofishin Kasafin Kuɗaɗen Tarayya ya nuna yadda Ma’aikatun Gwamnati, Hukumomi, Cibiyoyi da Rassan Ma’aikatu suka yi amfani da kashi 81 bisa 100 na kuɗaɗen da aka sakar masu domin aiwatar da manyan ayyukan rasa ƙasa.

Ya ce hakan na nuni da yadda Yakubu da ofishin sa ke nuna ƙwarewar iya aiki tare kuma da kishin fito da ƙa’idar aikin kashe kuɗaɗen shigar gwamnati a fili wajen fayyace komai dalla-dalla, ƙeƙe-da-ƙeƙe, ba tare da nuƙu-nuƙu ba.

“A ƙarƙashin Tanimu Yakubu, Ofishin Kasafin Kuɗaɗen Tarayya ya sake fasalin yadda ake sa-ido kan kuɗaɗen gwamnati.

“Domin a yanzu abin da muke gani akwai daidaito tsakanin kuɗaɗen kasafin kuɗaɗen da gwamnati ke fitarwa, yawan ayyukan da ake yi da kuɗaɗen da kuma sakamakon da al’umma ‘yan Nijeriya za su iya bin-diddigin tabbatarwa da idon su,” iji NFTD.

Sannan kuma an bayyana kasafin 2024 cewa yana ɗaya daga cikin kasafin da aka fi tsetstsefewa, aka aiwatar da shi filla-filla ba tare da ƙumbiya-ƙumbiya ko rufa-rufa ba a cikin shekarun nan.

“Musamman yadda Ofishin Kasafin Kuɗaɗen Tarayya ɗin ke fitar da rahotanni bayan kowane watanni ukun cikin shekara, wato sau huɗu kenan a cikin shekara. Kuma ake bugawa tare da wallafa rahotannin a fili kowa na gani.”

Sanarwar ta ce yadda Ofishin Kasafin Kuɗaɗen Tarayya a ƙarƙashin Yakubu ke baje bayanan kasafin kuɗaɗe a fili, hakan ya ƙara cusa wa jama’a samun yaƙini da gamsuwa kan yadda ake tafiyar da gwamnati a fannin kashe kuɗaɗen al’umma. Kuma hakan yana ƙara wa kasafin ƙima da darajar gamsuwa da shi.

Tags: Tanimu Yakubu
Previous Post

Nijeriya ta nemi haɗin gwiwa da sauran ƙasashe don ƙaryata labaran ƙarya

Next Post

CBN ya yi farin cikin cire Nijeriya daga ƙasashen da FATF ke kaffa-kaffar hada-hadar kuɗaɗe da su

Related Posts

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Shawarar CBN ga gwamnatocin jihohi: “A kiyaye bin ƙa’idojin kashe kuɗaɗe, a daina ciwo bashin alaƙaƙai

May 12, 2026
Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Lamiɗo Yuguda, sabon Mataimakin Gwamnan CBN ya shiga ofis

May 12, 2026
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Ƙwaƙudumar kasa biyan tulin bashin da manyan bankuna suka bayar laifin daraktoci da manyan masu hannayen jarin su ne, ba laifin CBN ba

May 8, 2026
Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tsauraran matakai da ƙa’idojin da CBN ya gindaya, dangane da bashin naira tiriliyan 2.9 da kamfanin Nestoil ya kasa biyan wasu bankunan Nijeriya

May 7, 2026
Manyan nasarorin da CBN ya samu cikin 2025
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Yadda ƙarfin laƙani da dafa’in CBN ke hana girgizar tattalin arzikin duniya yi wa Nijeriya barazana

May 6, 2026
Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris
Kuɗi Da Tattalin Arziki

Tinubu ya gana da manyan masu zuba jari na duniya a Paris

May 5, 2026
Next Post
Yadda tsare-tsaren CBN ke daƙile hauhawar farashi da tsadar rayuwa

CBN ya yi farin cikin cire Nijeriya daga ƙasashen da FATF ke kaffa-kaffar hada-hadar kuɗaɗe da su

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!