Shugaban Amurka Donald Trump ya amince cewa ana kashe Musulmi ma a Nijeriya, amma ya jaddada cewa Kiristoci ne ke kasancewa manyan waɗanda ake kai wa hare-haren tashin hankali, tare da gargaɗin cewa Amurka na iya kai ƙarin hare-haren soji idan irin wannan tashin hankalin ya ci gaba.
Trump ya yi waɗannan kalamai ne a wata hira da jaridar The New York Times da aka wallafa a ranar Alhamis, yayin da yake amsa tambayoyi kan wani harin sojin Amurka da aka kai a ranar Kirsimeti a Nijeriya.
Sojojin Amurka sun ce harin ya nufi ‘yan ƙungiyar Islamic State (ISIS) ne a arewa-maso-yammacin Nijeriya, kuma an gudanar da shi ne bisa buƙatar gwamnatin Nijeriya. Amma hukumomin Nijeriya sun bayyana lamarin a matsayin “aikin haɗin gwiwa” kan “’yan ta’adda,” suna jaddada cewa ba a kai harin ne kan wata ƙungiya ta addini ta musamman ba.
“Ina so ya zama hari na lokaci guda,” inji Trump. “Amma idan suka ci gaba da kashe Kiristoci, to zai zama hare-hare masu yawa.”
Da aka tambaye shi ya mayar da martani ga kalaman mai ba shi shawara kan harkokin Afrika cewa ‘yan ISIS da Boko Haram suna kashe Musulmi fiye da Kiristoci, sai Trump ya ce: “Ina ganin ana kashe Musulmi ma a Najeriya. Amma mafi yawanci Kiristoci ne.”
A ƙarshen watan Oktoba, Trump ya fara gargaɗi a bainar jama’a cewa Kiristanci na fuskantar abin da ya kira “barazanar wanzuwa” a Nijeriya, yana zargin gwamnatin Nijeriya da gaza kare al’ummomin Kiristoci yadda ya kamata, tare da barazanar sojin Amurka za su sa hannu.
Nijeriya, ƙasa mafi yawan jama’a a Afrika wadda ke da sama da mutane miliyan 230, kusan rabi-rabi ce tsakanin Kiristoci, waɗanda galibi suke a kudu, da Musulmi, waɗanda suka fi yawa a arewa.
Duk da ƙalubalen tsaro da ke ci gaba da addabar ƙasar, ciki har da tashe-tashen hankula na ‘yan tawaye, ‘yan bindiga da sace-sace, hukumomin Nijeriya sun sha yin watsi da iƙirarin cewa ana zaluntar Kiristoci da gangan. Gwamnatin ta jaddada cewa hare-haren ‘yan tawaye sun hallaka Musulmi da Kiristoci baki ɗaya.
Duk da cewa Nijeriya ta nuna shirin ta na haɗa kai da Amurka wajen yaƙi da ƙungiyoyin ‘yan tada ƙayar baya, ta nuna adawa sosai da ra’ayoyin da ke nuna cewa tashin hankalin a ƙasar na shafar Kiristoci kaɗai ne.
(Reuters)







