• Gida
  • Labarai
  • Ƙasashen Duniya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Siyasa
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Mahanga
  • Rahoton Musamman
  • Wasanni
Tuesday, May 5, 2026
New Citizen Hausa
  • Login
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni
No Result
View All Result
New Citizen Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Siyasa

Tinubu yana kafa ginshiƙin cigaba mai ɗorewa tare da inganta rayuwar jama’a, inji Ministan Yaɗa Labarai

ABUBAKAR IBRAHIM by ABUBAKAR IBRAHIM
January 16, 2026
in Siyasa
A A
0
Tinubu yana kafa ginshiƙin cigaba mai ɗorewa tare da inganta rayuwar jama’a, inji Ministan Yaɗa Labarai
Daga hagu: Jagoran ƙungiyar 'Grassroot Advocacy for Tinubu 2027' (GAT) na Ƙasa, Farfesa Ochugudu Achoda Ipuele, yana miƙa takardar naɗin Uban Ƙungiya ga Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, a lokacin ziyarar a ranar Alhamis a Abuja. (Hoto daga: Khalid Ahmed)

Daga hagu: Jagoran ƙungiyar 'Grassroot Advocacy for Tinubu 2027' (GAT) na Ƙasa, Farfesa Ochugudu Achoda Ipuele, yana miƙa takardar naɗin Uban Ƙungiya ga Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, a lokacin ziyarar a ranar Alhamis a Abuja. (Hoto daga: Khalid Ahmed)

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yana kafa ginshiƙin mai ƙarfi domin samun cigaba mai ɗorewa tare kuma da bunƙasar tattalin arziki ga kowa, ta hanyar ɗaukar tsauraran matakai.

Idris ya bayyana hakan ne ranar Alhamis a Abuja yayin da yake karɓar baƙuncin membobin ƙungiyar fafutikar sake zaɓen Tinubu mai suna ‘Grassroots Advocacy for Tinubu (GAT) 2027’, waɗanda suka kai masa ziyarar ban-girma.

A cewar ministan, gwamnatin ta ɗauki wasu matakai masu tsauri amma masu muhimmanci domin daidaita tattalin arzikin ƙasar nan, inda ya bayyana cewa tuni alamun farfaɗowa suka fara bayyana a sassa daban-daban na tattalin arziki.

Ya ce: “An ɗauki waɗannan matakai ne domin daidaita tattalin arziki da maido da ƙwarin gwiwa. Abin da muke gani a yau shi ne ginshiƙin cigaba mai ɗorewa da kuma wadata da za ta amfani kowa.”

Ya jaddada cewa dole ne a kare kyakkyawan yanayin tattalin arzikin da Nijeriya ke ciki ta hanyar haɗin kai, yaɗa labarai cikin gaskiya, da kuma goyon bayan manufofin gwamnati baki ɗaya.

Ya yi gargaɗin cewa yaɗa labaran ƙarya ko ɓata sunan ƙasa yana iya karya gwiwar masu zuba jari tare da daƙile cigaba.

“Dole ne mu faɗi alheri kuma mu faɗi gaskiya game da Nijeriya,” inji shi. “Idan muka nuna daidaito da haɗin kai, za mu jawo hankalin masu zuba jari sannan mu samar wa mutanen mu damarmaki.”

Idris ya yaba wa ‘ya’yan ƙungiyar GAT bisa jajircewar su wajen wayar da kan jama’a, inda ya kuma amince da shawarar ƙungiyar na yin haɗin gwiwa da Ma’aikatar Yaɗa Labarai wajen faɗakar da jama’a, jawo matasa a jiki, da kuma kyakkyawan tsarin yaɗa labarai.

Ya sake jaddada ƙudirin Shugaban Ƙasa Tinubu na gina Nijeriyar da za ta amfani kowa, ba tare da la’akari da addini ko yanki ba, yana mai cewa haɗin kan ƙasa shi ne jigon hangen nesa na wannan gwamnati.

Shi ma a nasa jawabin, jigo a ƙungiyar GAT, Farfesa Ochugudu Achoda Ipuele, ya ce sun kai ziyarar ne domin yi wa ministan bayani kan ayyukan ƙungiyar da kuma nuna goyon baya ga aikin sa na sanar da ’yan Nijeriya gaskiyar manufofin gwamnati.

Ya ce: “Mun zo nan ne don mu taya ku murnar wannan babban nauyi da kuke ɗauke da shi ga Nijeriya, wanda shi ne sanar da ƙasa, fito da manufofin gwamnati fili, da kuma kai sahihan bayanai zuwa ga talakawa.”

Ya ƙara da cewa ƙungiyar ta himmatu wajen kare manufofin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ta hanyar ƙalubalantar labaran ƙarya, musamman a lokutan zaɓe, da kuma jawo matasa a jiki.

Farfesa Ipuele ya ce: “Wannan ƙungiya a shirye take ta mayar da martani nan take kan duk wani labarin ƙarya, tare da haɗa kai da matasa, domin ganin cewa yayin da muke tunkarar shekarar 2027, Shirin Sabunta Fata ya ci gaba tare da samar da ƙarin shirye-shirye ga ƙasa.”

Tags: FarfesaOchuguduAchodaIpueleGATMohammedIdriszaben2027
Previous Post

Ilimin ‘ya mace: Fiye da ‘yan mata 40,000 a Kaduna sun amfana da shirin koyon dabarun rayuwa na Gwamna Uba Sani

Next Post

Tinubu ya yi jimamin rasuwar limamin da ya ceci Kiristoci sama da 200 a Filato

Related Posts

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista
Siyasa

Shugaban NDC, Dickson ya yi wa Umar Arɗo raddi kan barazanar kai su kotu kan batun rajista

May 5, 2026
Kwankwaso da Obi sun koma NDC
Siyasa

Kwankwaso da Obi sun koma NDC

May 3, 2026
Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi
Siyasa

Dalili na na ficewa daga ADC – Peter Obi

May 3, 2026
Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC
Siyasa

Binani ta fice daga ADC ta koma NDC watanni tara bayan barin APC

May 1, 2026
Rikicin shugabanci a ADC: Ɓangaren David Mark ya rubuta wa CJN takarda, ya roƙi a gaggauta yanke hukunci
Siyasa

Rikicin shugabanci a ADC: Ɓangaren David Mark ya rubuta wa CJN takarda, ya roƙi a gaggauta yanke hukunci

April 28, 2026
A taron Ibadan, ‘yan adawa sun haɗa kai, sun amince da tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda ɗaya a zaɓen 2027
Siyasa

A taron Ibadan, ‘yan adawa sun haɗa kai, sun amince da tsayar da ɗan takarar shugaban ƙasa guda ɗaya a zaɓen 2027

April 25, 2026
Next Post
Tinubu ya yi jimamin rasuwar limamin da ya ceci Kiristoci sama da 200 a Filato

Tinubu ya yi jimamin rasuwar limamin da ya ceci Kiristoci sama da 200 a Filato

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

No Result
View All Result

Archives

  • May 2026
  • April 2026
  • March 2026
  • February 2026
  • January 2026
  • December 2025
  • November 2025
  • October 2025
  • September 2025
  • August 2025
  • July 2025
  • May 2025
  • April 2025
  • March 2025
  • October 2024

Categories

  • Hotuna
  • Ilimi
  • Kiwon Lafiya
  • Kuɗi Da Tattalin Arziki
  • Labarai
  • Mahanga
  • Nishaɗi Da Al'adu
  • Rahoton Musamman
  • Siyasa
  • Tsaro
  • Wasanni
  • Ƙasashen Duniya
No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Ƙasashen Duniya
    • Ilimi
    • Kiwon Lafiya
    • Rahoton Musamman
    • Kuɗi Da Tattalin Arziki
    • Mahanga
  • Siyasa
  • Nishaɗi Da Al’adu
  • Wasanni

© 2024 New Citizen

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In
error: Content is protected !!